< Psaltaren 29 >

1 En Psalm Davids. Bärer fram Herranom, I väldige; bärer fram Herranom äro och starkhet.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Bärer fram Herranom hans Namns äro; tillbedjer Herran i heligo prydning.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Herrans röst går på vattnen; ärones Gud dundrar; Herren på stor vatten.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 Herrans röst går med magt; Herrans röst går härliga.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 Herrans röst sönderbryter cedrer; Herren sönderbryter cedrer i Libanon;
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Och låter dem springa såsom en kalf; Libanon och Sirion, såsom en ung enhörning.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Herrans röst afhugger såsom en eldslåge.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 Herrans röst berörer öknena; Herrans röst berörer öknena Kades.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Herrans röst berörer hinderna, och blottar skogarna; och i hans tempel skall hvar och en säga honom äro.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Herren sitter till att göra ena flod, och Herren blifver en Konung i evighet.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Herren skall gifva sino folke kraft; Herren skall välsigna sitt folk med frid.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psaltaren 29 >