< Psaltaren 132 >
1 En visa i högre choren. Tänk, Herre, uppå David, och uppå allt hans lidande;
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 Hvilken Herranom svor, och lofvade dem mägtiga i Jacob:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 Jag vill icke gå i mins hus hyddo, eller lägga mig på mine sängs lägre;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 Jag vill icke låta mina ögon sofva, eller mina ögnalock sömnoga vara;
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 Tilldess jag må finna ett rum för Herranom, till en boning dem mägtiga i Jacob.
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Si, vi höre derom i Ephrata; vi hafve funnit det på skogsmarkene.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Vi vilje gå in uti hans boningar, och tillbedja inför hans fotapall.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Herre, statt upp till dina ro, du och din magts ark.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Låt dina Prester kläda sig med rättfärdighet, och dina heliga glädja sig.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Tag icke bort dins smordas regemente, for din tjenare Davids skull.
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Herren hafver svorit David en sannan ed, der skall han intet ifrå träda: Jag skall sätta dig dins lifs frukt uppå din stol.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Om dina barn hålla mitt förbund, och min vittnesbörd, som jag dem lärandes varder, så skola ock deras barn sitta på dinom stol evinnerliga.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Ty Herren hafver utvalt Zion, och hafver lust till att bo der.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 Detta är min hvila evinnerliga, här vill jag bo; ty här behagar mig väl.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Jag vill välsigna dess spis, och gifva dess fattigom bröd nog.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Dess Prester vill jag bekläda med salighet, och dess helige skola glädja sig.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Dersammastäds skall uppgå Davids horn; jag hafver tillredt minom smorda ena lykto.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Hans fiendar vill jag bekläda med skam; men öfver honom skall hans krona blomstras.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”