< Obadja 1 >

1 Detta är Obadia syn. Så säger Herren Herren om Edom: Vi hafve hört af Herranom, att ett bådskap är sändt ibland Hedningarna: Upp, och låter oss örliga emot dem.
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Si, jag hafver gjort dig ringa ibland Hedningarna, och mycket föraktad.
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 Dins hjertas högmod hafver bedragit dig, efter du bor uti stenklyftor, på din höga slott, och säger i dino hjerta: Ho vill drifva mig här neder?
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 Om du än fore uppe i höjdene, lika som en örn, och gjorde ditt näste ibland stjernorna, så vill jag likväl draga dig der neder, säger Herren.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 Om tjufvar eller förhärjare komma om nattena öfver dig, o! huru tyst skall du då varda; ja, de skola nog stjäla; och om vinhemtare öfver dig komma, så skola de icke lefva dig någon efterhemtning.
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 O! huru skola de utransaka Esau, och uppsöka hans håfvor.
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 Alle de, som i förbund med dig äro, de skola drifva dig bort utu landet; de män der du sätter din tröst till, de skola bedraga dig, och öfverfalla dig; de som äta ditt bröd, de skola förråda dig, förr än du vetst der något af.
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 Hvad gäller, säger Herren, jag skall på den tiden nederlägga de visa i Edom, och den klokhet på Esau berg.
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 Ty dine starke i Theman skola förtvifla, på det de alle skola förgås genom mord, på Esau berg.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 För den orätts skull, som emot din broder Jacob bedrifven vardt, skall du på all skam komma, och till evig tid förlagd varda.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 Den tid, då du emot honom stod, då främmande bortförde hans här fångnan, och utländningar drogo in igenom hans portar, och kastade lott öfver Jerusalem, då vast du lika som en af dem.
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 Du skall intet mer se dina lust på dinom broder, i hans eländes tid, och skall icke mer glädja dig öfver Juda barn, i deras jämmers tid; och skall icke tala så stolt ord med din mun, i deras ångests tid.
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 Du skall icke indraga genom mins folks portar, i deras jämmers tid; du skall icke se dina lust på deras olycko, uti deras jämmers tid; du skall icke sända emot deras här, uti deras jämmers tid.
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 Du skall icke stå i vägaskäl, till att mörda deras flyktiga; du skall icke förråda deras qvarblefna, i deras ångests tid.
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 Ty Herrans dag är hardt när öfver alla Hedningar. Lika som du gjort hafver, så skall dig ske igen; och såsom du förtjent hafver, så skall det komma dig uppå ditt hufvud igen.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 Ty lika som I på mitt helga berg druckit hafven, så skola alle Hedningar dricka allt framgent; ja, de skola utsupat och uppsvälgat, att det skall vara lika som der aldrig något varit hade.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 Men på Zions berg skola ännu somlige hulpne varda; de skola vara en helgedom, och Jacobs hus skall besitta sina besittare.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 Och Jacobs hus skall en eld varda, och Josephs hus en låge, men Esau hus strå; de skola upptända och förtära det, så att Esau huse intet skall qvart blifva; ty Herren hafver det talat.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 Och de söderut skola, besitta Esau berg, och de i dalomen skola besitta de Philisteer; ja, de skola besitta Ephraims mark, och Samarie mark; och BenJamin Gileads berg.
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 Och de fördrefne af denna Israels barnas här, hvilke ibland de Cananeer allt intill Zarpath äro, och de fördrefne af Jerusalems stad, hvilke i Sepharad äro, skola besitta de städer söderut.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 Och frälsare skola uppkomma på Zions berg, till att döma Esau berg. Alltså skall då riket vara Herrans.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Obadja 1 >