< Nehemja 3 >

1 Och Eljasib, öfverste Presten, stod upp med sina bröder Presterna, och byggde fåraporten; honom helgade de, och satte in hans dörrar; men de helgade honom allt intill det tornet Mea, nämliga allt intill det tornet Hananeel.
Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
2 Bredevid dem byggde de män af Jericho; och näst dem byggde Saccur, Imri son.
Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
3 Men fiskaporten byggde Senaa barn; honom täckte de, och satte in hans dörrar, lås och bommar.
’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
4 Näst dem byggde Meremoth, Uria son, Hakkoz sons; näst dem byggde Mesullam, Berechia son, Mesesabeels sons; näst dem byggde Zadok, Baana son.
Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
5 Näst dem byggde de af Thekoa; men deras väldige böjde icke sin hals till sins herras tjenst.
Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
6 Den gamla porten byggde Jojada, Paseahs son, och Mesullam, Besodeja son; honom täckte de, och satte in hans dörrar, och lås och bommar.
Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
7 Näst dem byggde Melatia af Gibeon, och Jadon af Merono, män af Gibeon och Mizpa, på landshöfdingans säte, på denna sidon älfven.
Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
8 Näst efter honom byggde Ussiel, Harhaja son, guldsmeden; näst honom byggde Hanania, apothekarens son, och de förstärkte Jerusalem allt intill de breda murar.
Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
9 Näst honom byggde Rephaja, Hurs son, öfversten öfver en half fjerding af Jerusalem.
Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
10 Näst honom byggde Jedaja, Harumaphs son, tvärtöfver sitt hus; näst honom byggde Hattus, Hasabenja son.
Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
11 Men Malchija, Harims son, och Hasub, Pahath Moabs son, byggde ett annat stycke, och tornet med ugnarna.
Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
12 Näst honom byggde Sallum, Halohes son, öfversten för en half fjerding i Jerusalem, han och hans döttrar.
Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
13 Dalporten byggde Hanun och borgarena af Sanoah; de byggde honom, och satte in hans dörrar, och lås och bommar, och tusende alnar på murenom allt intill dyngoporten.
Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
14 Men dyngoporten byggde Malchija, Rechabs son, öfversten i vingårdsmännernas fjerding; han byggde honom, och satte in hans dörrar, lås och bommar.
Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
15 Brunnporten byggde Sallum, CholHose son, en öfverste för en fjerding i Mizpa; han byggde honom, och täckten, och satte in hans dörrar, lås och bommar; dertill ock murarna vid dammen Selah, vid Konungsörtagården, allt intill trapporna, som gå nederåt ifrå Davids stad.
Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
16 Näst honom byggde Nehemia, Asbuks son, öfversten för den halfva fjerdingen i BethZur, allt intill gentemot Davids grafvar, och allt intill den dammen Asuja, och allt intill de väldigas hus.
Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
17 Efter honom byggde de Leviter, Rehum, Bani son; bredevid honom byggde Hasabia, öfversten för halfva fjerdingen i Kegila, i hans fjerding.
Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
18 Efter honom byggde deras bröder Bavai, Henadads son, öfversten för en half fjerding i Kegila.
Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
19 Efter honom byggde Eser, Jesua son, öfversten i Mizpa, ett annat stycke, inåt harneskhushörnet.
Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
20 Efter honom, uppå berget, byggde Baruch, Sabbi son, ett annat stycke, ifrå hörnet allt intill Eljasibs öfversta Prestens husdörr.
Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
21 Efter honom byggde Meremoth, Uria son, Hakkoz sons, ett annat stycke, ifrån Eljasibs husdörr, allt intill ändan af Eljasibs hus.
Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
22 Efter honom byggde Presterna, de män af landsbygdene.
Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
23 Efter dem byggde BenJamin och Hasub, tvärsöfver deras hus; efter dem byggde Asaria, Maaseja son, Anania sons, jemte sitt hus.
Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
24 Efter honom byggde Binnui, Henadads son, ett annat stycke, ifrån Asaria hus intill båget, och allt intill hörnet;
Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
25 Palal, Usai son, emot båget, och det höga tornet, som synes utaf Konungshuset, vid fångahusens gård; efter honom Pedaja, Paros son.
sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
26 Men de Nethinim bodde uti Ophel, allt intill vattuporten österut, der tornet ut synes.
da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
27 Efter dem byggde de af Thekoa ett annat stycke, tvärtemot det stora tornet, som ut synes, allt intill murarna Ophel.
Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
28 Men ifrå hästaporten byggde Presterna, hvardera emot sitt hus.
Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
29 Efter dem byggde Zadok, Immers son, emot sitt hus; efter honom byggde Semaja, Sechania son, den dörravaktaren, östantill.
Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
30 Efter honom byggde Hanania, Selemia son, och Hanun, Zalaphs son, den sjette, ett annat stycke; efter honom byggde Mesullam, Berechia son, emot sin fatabur.
Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
31 Efter honom byggde Malchija guldsmedssonen, allt intill de Nethinims och krämares hus, emot rådsporten, och intill hörnsalen.
Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
32 Och emellan hörnsalen allt intill fåraporten byggde guldsmederna och krämarena.
Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.

< Nehemja 3 >