< Nahum 1 >

1 Detta är tungen öfver Nineve, och Nahums Propheties bok af Elkos.
Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.
2 Gud är nitisk, och Herren är en hämnare; ja, en hämnare är Herren, och grym. Herren är en hämnare uppå sina fiendar, och den der sina ovänner intet förgäter.
Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya kuma. Ubangiji Allah mai kishi ne, mai ɗaukar fansa kuma. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa, yakan ci gaba da fushi a kan abokan gābansa.
3 Herren är tålig, och af stora magt, och låter intet ostraffadt blifva. Han är Herren, hvilkens vägar äro uti väder och storm, och tjockt moln under hans fötter;
Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai iko duka kuma. Ubangiji ba zai bar masu zunubi babu horo ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da kuma hadari, gizagizai kuwa su ne ƙurar ƙafafunsa.
4 Den som näpser hafvet, och förtorkar det, och uttorkar alla floder; Basan och Carmel försmäkta, och hvad som blomstras på Libanons berg, det måste försmäkta för honom.
Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.
5 Bergen bäfva för honom, och högarna förgås; jorden darrar för honom; dertill jordenes krets, och alle de som bo der uppå.
Duwatsu suna rawan jiki a gabansa tuddai kuma sun narke. Duniya da dukan abin da yake cikinta suna rawan jiki a gabansa.
6 Ho kan blifva ståndandes för hans vrede? Och ho kan blifva för hans grymhet? Hans vrede brinner såsom en eld, och hällebergen remna för honom.
Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa yake da ikon jimre wa zafin hasalarsa? Ana zuba fushinsa kamar wuta; aka kuma ragargaza duwatsu a gabansa.
7 Herren är mild, och ett fäste uti nödenes tid; och känner dem som trösta uppå honom.
Ubangiji nagari ne, mafaka kuma a lokacin wahala. Yana kula da waɗanda suka dogara gare shi,
8 När floden löper öfver, så gör han en ända med henne; men sina fiendar förföljer han med mörker.
amma da ambaliyar ruwa zai kawo Ninebe ga ƙarshe; zai fafari maƙiyansa zuwa cikin duhu.
9 Hvad är då det, som I tagen eder före emot Herran? Han låter del dock intet af varda; ty bedröfvelsen skall icke vara evinnerliga.
Dukan abin da suke ƙullawa game da Ubangiji zai kawo ga ƙarshe; wahala ba za tă sāke komowa ƙaro na biyu ba.
10 Ty lika som när törne, de ännu om hvartannat växa, och bästa musten hafva, varda uppbränd såsom hel torr strå;
Za su sarƙafe a ƙaya, za su kuma bugu da ruwan inabinsu; za a laƙume su kamar busasshiyar ciyawa.
11 Alltså varder det skalkarådet, som af dig kommer, ondt tänkandes emot Herran.
Daga cikinki, ya Ninebe wani ya fito wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci yana ba da mugayen shawarwari.
12 Detta säger Herren: De komme så tillrustade och mägtige som de vilja, så skola de likväl omkullhuggne varda, och gå sin kos; ty jag vill ödmjuka dig, men dock icke platt förderfva dig;
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Ko da yake sun yi tarayya, suna kuma da yawa, za a yanke su, a kawar a su. Ko da yake na ba ki azaba, ya Yahuda, ba zan ƙara ba ki azaba ba.
13 Utan vill då kasta hans ok, som du drager, ifrå dig och slita din band sönder.
Yanzu zan karya karkiyarsu daga wuyanki in kuma tsittsinke sarƙar da suka ɗaura ki.”
14 Men emot dig hafver Herren budit, att ingen dins namns säd mer blifva skall. Uti dins guds huse vill jag förgöra dig; jag skall gifva dig ena graf ibland afgudar och beläte, och du måste till skam varda.
Ubangiji ya ba da umarni game da ke Ninebe, “Ba za ki sami zuriyar da za tă ci gaba da sunanki ba. Zan rurrushe siffofin da kuka sassaƙa da kuma gumakan da kuka ƙera gumakan da suke a cikin haikalin allolinku. Zan shirya kabarinki, domin ke muguwa ce.”
15 Si, på bergen komma ens god bådskaps fötter, den der god tiden de bär: Håll dina högtider, Juda, och betala din löfte; ty skalken skall icke mer komma öfver dig; det är platt ute med honom.
Duba, can a bisa duwatsu, ga ƙafafu mai kawo labari mai daɗi, wanda yake shelar salama! Ki yi bukukkuwanki, ya Yahuda, ki kuma cika wa’adodinki. Mugaye ba za su ƙara mamaye ki ba; domin za a hallaka su ƙaƙaf.

< Nahum 1 >