< Matteus 1 >

1 Detta är boken af Jesu Christi börd, hvilken som är Davids son, Abrahams sons.
Littafin asalin Yesu Almasihu Dan Dauda, Dan Ibrahim.
2 Abraham födde Isaac; Isaac födde Jacob; Jacob födde Juda, och hans bröder.
Ibrahim shine mahaifin Ishaku, Ishaku shine mahaifin Yakubu, Yakubu shine mahaifin Yahuza da 'yan'uwansa.
3 Juda födde Pharez och Zara, af Thamar; Pharez födde Hezrom; Hezrom födde Aram.
Yahuza shine mahaifin Farisa da Zera, ta wurin Tamar. Farisa kuma shine mahaifin Hasruna, Hasruna kuma shine mahaifin Aram.
4 Aram födde Aminadab; Aminadab födde Nahasson; Nahasson födde Salmon.
Aram shine mahaifin Amminadab, Amminadab shine mahaifin Nashon, Nashon shine mahaifin Salmon.
5 Salmon födde Boas, af Rahab; Boas födde Obed, af Ruth; Obed födde Jesse.
Salmon shine mahaifin Bo'aza ta wurin Rahab, Bo'aza shine mahaifin Obida ta wurin Rut. Obida shine mahaifin Yesse,
6 Jesse födde Konung David; Konung David födde Salomon, af henne som var Urie hustru.
Yesse shine mahaifin sarki Dauda. Sarki Dauda shine mahaifin Sulaimanu ta wurin matar Uriya.
7 Salomon födde Roboam; Roboam födde Abia; Abia födde Asa.
Sulaimanu shine mahaifin Rehobo'am, Rehobo'am shine mahaifin Abija, Abija shine mahaifin Asa.
8 Asa födde Josaphat; Josaphat födde Joram; Joram födde Osia.
Asa shine mahaifin Yehoshafat, Yehoshafat shine mahaifin Yoram, Yoram kuma shine mahaifin Uziya.
9 Osia födde Joatham; Joatham födde Achas; Achas födde Ezechia.
Uziya shine mahaifin Yotam, Yotam shine mahaifin Ahaz, Ahaz shine mahaifin Hezekiya.
10 Ezechia födde Manasse; Manasse födde Amon; Amon födde Josia.
Hezekiya shine mahaifin Manassa, Manassa shine mahaifin Amon, sannan Amon shine mahaifin Yosiya.
11 Josia födde Jechonia och hans bröder, vid det Babyloniska fängelset.
Yosiya shine mahaifin Yekoniya da 'yan'uwansa, dai dai locacin da aka kwashe su zuwa kasar Babila.
12 Men efter det Babyloniska fängelset födde Jechonia Salathiel; Salathiel födde Zorobabel.
Bayan kwasar su zuwa kasar Babila, Yekoniya shine mahaifin Sheyaltiyel, Sheyaltiyel shine mahaifin Zarubabel.
13 Zorobabel födde Abiud; Abiud födde Eliakim; Eliakim födde Asor.
Zarubabel shine mahaifin Abihudu, Abihudu shine mahaifin Eliyakim, sannan Eliyakim shine mahaifin Azuru.
14 Asor födde Zadok; Zadok födde Achim; Achim födde Eliud.
Azuru shine mahaifin Saduku. Saduku shine mahaifin Akimu, sannan Akimu shine mahaifin Aliyudu
15 Eliud födde Eleazar: Eleazar födde Mattham; Mattham födde Jacob.
Aliyudu shine mahaifin Ali'azara, Ali'azara shine mahaifin Matana, sannan Matana shine mahaifin Yakubu.
16 Jacob födde Joseph, Marie man, af hvilko är födder Jesus, som kallas Christus.
Yakubu shine mahaifin Yusufu maigidan Maryamu, wadda ta wurin ta ne aka haifi Yesu, wanda ake ce da shi Almasihu.
17 Så äro alle lederna, ifrån Abraham intill David, fjorton leder; ifrå David till det Babyloniska fängelset, ock fjorton leder; ifrå det Babyloniska fängelset intill Christum, ock fjorton leder.
Tun daga Ibrahim zuwa Dauda, an yi tsara goma sha hudu ne, daga Dauda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa Babila, tsara goma sha hudu ne, sannan daga lokacin da aka kwashe su zuwa Babila zuwa Almasihu tsara goma sha hudu ne
18 Jesu Christi födelse gick så till: När Maria, hans moder, var trolofvad Joseph, förr än de kommo samman, fans hon vara hafvandes af den Heliga Anda.
Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu ta kasance. Mahaifiyarsa, Maryamu, tana tashi da Yusufu, amma kafin su yi aure, sai aka same ta da juna biyu ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
19 Men efter Joseph var en from man, och ville icke röja henne, tänkte han hemliga öfvergifva henne.
Mijinta, Yusufu, adalin mutum ne, amma ba ya so ya kunyatar da ita a sarari. Sai ya yi shawara ya sake ta a asirce.
20 När han detta tänkte, si, då uppenbarades honom i sömnen Herrans Ängel, och sade: Joseph, Davids son, räds icke taga Maria, din hustru, till dig; ty det som är afladt i henne, det är af den Heliga Anda.
Yana cikin tunanin wadannan al'amura, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gareshi a mafarki, ya ce masa, “Yusufu, dan Dauda, kada ka ji tsoron daukar Maryamu a matsayin matarka. Gama abinda ke cikinta, ta wurin Ruhu Mai Tsarki aka same shi.
21 Och hon skall föda en Son, och du skall kalla hans Namn JESUS; ty han skall frälsa sitt folk ifrå deras synder.
Za ta haifi Da, za ka kira sunansa Yesu, domin za ya ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 Detta är allt skedt, på det fullbordas skulle det af Herranom sagdt är genom Propheten, som sade:
Duk wannan ya faru ne domin a cika abinda aka fada ta bakin annabin, cewa,
23 Si, en Jungfru skall varda hafvandes, och föda en Son, och de skola kalla hans Namn EmmanuEl; det är så mycket sagdt: Gud med oss.
“Duba, budurwa za ta sami juna biyu sannan za ta haifi da, za su kira sunansa Immanuel”-ma'ana, “Allah tare da mu.”
24 När Joseph vaknade upp af sömnen, gjorde han som Herrans Ängel hade honom befallt, och tog sina hustru till sig.
Yusufu ya farka daga barci, ya yi kamar yadda mala'ikan Ubangiji ya umarce shi, sai ya dauke ta a matsayin matarsa.
25 Och kände henne intet, tilldess hon födde sin första Son; och kallade hans Namn JESUS.
Amma Yusufu bai sadu da ita ba sai bayan da ta haifi da. Ya kira sunansa Yesu.

< Matteus 1 >