< Lukas 1 >

1 Efter månge hafva tagit sig före att beskrifva de ting, som ibland oss aldravissast äro;
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 Såsom de oss sagt hafva, som af begynnelsen det med sin ögon sågo, och sjelfve en del voro af det de sade;
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 Syntes ock mig, sedan jag af begynnelsen all ting granneliga utfrågat hafver, ordenteligen skrifva dig till, min gode Theophile;
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 Att du må förfara vissa sanningen om de stycker, der du om undervister äst.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 Uti Herodis, Judee Konungs, tid, var en Prest, utaf Abie skifte, benämnd Zacharias; och hans hustru, af Aarons döttrar, benämnd Elisabet.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 De voro både rättfärdige för Gud, vandrande i all Herrans bud och stadgar ostraffeliga.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 Och de hade inga barn; ty Elisabet var ofruktsam, och både voro de framlidne i sin ålder.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 Så begaf det sig, då han i sitt skifte skulle hålla sitt Prestaämbete för Gudi,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 Efter Presterskapets sed, och det föll på honom, att han skulle upptända rökelse, gick han in i Herrans tempel;
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 Och allt folket var utantill, och bad, så länge rökelsen skedde.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 Så syntes honom Herrans Ängel, ståndandes på högra sidon vid rökaltaret.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 Och Zacharias vardt förskräckt, då han såg honom, och en räddhåge föll öfver honom.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 Så sade Ängelen till honom: Var icke förfärad, Zacharia; ty din bön är hörd, och din hustru Elisabet skall föda dig en son, hvilkens namn du skall kalla Johannes.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 Och dig skall varda glädje och fröjd; och månge skola fröjdas af hans födelse;
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 Ty han skall varda stor för Herranom; vin och starka drycker skall han icke dricka; och skall straxt i moderlifvet uppfylld varda med den Helga Anda;
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 Och han skall omvända många af Israels barn till Herran, deras Gud.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 Och han skall gå för honom, med Elie anda och kraft, till att omvända fädernas hjerta till barnen, och de ohöriga till de rättfärdigas snällhet; och göra Herranom ett beredt folk.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Då sade Zacharias till Ängelen: Hvaraf skall jag detta veta? Ty jag är gammal, och min hustru är framliden i åldren.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 Ängelen svarade, och sade till honom: Jag är Gabriel, som står i Guds åsyn, och är utsänd till att tala dig till, och båda dig denna goda tidenden.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 Och si, du skall varda mållös, och skall intet kunna tala, intill den dagen, då detta sker; derföre, att du icke trodde minom ordom, hvilke skola fullkomnad varda i sin tid.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 Och folket förbidde Zachariam, och förundrade sig, att han så länge dvaldes i templet.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 Men då han utgick, kunde han intet tala med dem; och så förmärkte de, att han hade sett någon syn i templet; och han tecknade dem, och blef mållös.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 Och det begaf sig, då hans ämbetsdagar ute voro, gick han hem i sitt hus.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 Och efter de dagar vardt hans hustru Elisabet hafvandes; och fördolde sig i fem månader, och sade:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Så hafver nu Herren gjort med mig, i de dagar, då han såg till mig, på det han skulle borttaga min försmädelse ibland menniskorna.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 Uti sjette månaden vardt Gabriel Ängel utsänd af Gudi, uti en stad i Galileen, benämnd Nazareth;
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 Till en jungfru, som förlofvad var enom man, hvilkens namn var Joseph, af Davids hus; och jungfrunes namn Maria.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 Och Ängelen kom in till henne, och sade: Hel, full med nåd! Herren är med dig; välsignad du ibland qvinnor.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 Då hon såg honom, vardt hon förfärad af hans tal, och tänkte uppå, hurudana helsning detta var.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 Då sade Ängelen till henne: Frukta dig icke, Maria; ty du hafver funnit nåd för Gudi.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 Si, du skall afla i ditt lif, och föda en son, hvilkens Namn du skall kalla JESUS.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 Han skall varda stor, och kallas dens Högstas Son; och Herren Gud skall gifva honom hans faders Davids säte;
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 Och han skall vara en Konung öfver Jacobs hus i evig tid; och på hans rike skall ingen ände vara. (aiōn g165)
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
34 Då sade Maria till Ängelen: Huru skall detta tillgå? Ty jag vet af ingen man.
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 Ängelen svarade, och sade till henne: Den Helge Ande skall komma öfver dig, och dens Högstas kraft skall öfverskygga dig; derföre ock det Helga, som af dig födt varder, skall kallas Guds Son.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 Och si, Elisabet, din fränka, hafver ock aflat en son i sin ålderdom; och detta är sjette månaden åt henne, som hetes vara ofruktsam;
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Ty för Gud är ingen ting omöjelig.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 Då sade Maria: Si, Herrans tjenarinna; varde mig efter ditt tal. Och Ängelen skiljdes ifrå henne.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 Uti de dagar stod Maria upp, och gick i bergsbygdena med hast, uti Jude stad;
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 Och kom uti Zacharie hus, och helsade Elisabet.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 Och det begaf sig, då Elisabet hörde Marie helsning, sprang barnet uti hennes lif. Och Elisabet vardt uppfylld med den Helga Anda;
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 Och hon ropade med höga röst, och sade: Välsignad du ibland qvinnor, och välsignad dins lifs frukt.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Och hvadan kommer mig detta, att mins Herras moder kommer till mig?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 Si, då rösten af dine helsning kom i min öron, sprang barnet af glädje i mitt lif.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 Och salig äst du, som trodde; ty all ting varda fullbordad, som dig sagd äro af Herranom.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Och Maria sade: Min själ prisar storliga Herran;
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 Och min ande fröjdar sig i Gudi, minom Frälsare;
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 Ty han hafver sett till sine tjenarinnos ringhet: Si, härefter varda all slägte mig saliga kallande.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 Ty den Mägtige hafver gjort mägtig ting med mig, och hans Namn är heligt;
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 Och hans barmhertighet varar ifrå slägte till slägte, öfver dem som frukta honom.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Han hafver bedrifvit magt med sinom arm, och förskingrat dem, som högfärdige äro uti deras hjertas sinne.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 De mägtige hafver han satt af sätet, och uppsatt de ringa.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 De hungriga hafver han med god ting uppfyllt, och de rika hafver han låtit tomma blifva.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Han hafver upptagit sin tjenare Israel, tänkande på sina barmhertighet;
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 Såsom han sagt hafver till våra fäder, Abraham och hans säd, till evig tid. (aiōn g165)
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
56 Och Maria blef när henne vid tre månader; och gick så hem i sitt hus igen.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Så vardt då Elisabet tiden fullbordad att hon skulle föda, och hon födde en son.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Och hennes grannar och fränder fingo höra, att Herren hade gjort stor barmhertighet med henne, och fröjdade sig med henne.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 Och det begaf sig, på åttonde dagen kommo de till att omskära barnet; och kallade honom, efter hans fader, Zacharias.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 Då svarade hans moder, och sade: Ingalunda; men han skall heta Johannes.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 Då sade de till henne: Uti dine slägt är ingen, som hafver det namnet.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 Så tecknade de hans fader, hvad han ville kalla honom.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 Och han äskade ena taflo, der han uti skref, sägandes: Johannes är hans namn; och alle förundrade sig derpå.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 Och straxt öppnades hans mun, och hans tunga; och han talade, lofvandes Gud.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Och stor fruktan kom öfver alla deras grannar; och ryktet om allt detta gick ut öfver alla Judiska bergsbygdena.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 Och alle de, som det hörde, sattet i sitt hjerta, sägande: Hvad månn varda utaf detta barnet? Ty Herrans hand var med honom.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 Och hans fader Zacharias vardt uppfylld med den Helga Anda, propheterade, och sade:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Lofvad vare Herren, Israels Gud; ty han hafver besökt och förlossat sitt folk;
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 Och hafver upprättat oss salighetenes horn, uti sins tjenares Davids hus;
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 Såsom han i förtiden talat hafver, genom sina helga Propheters mun; (aiōn g165)
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
71 Att han skulle frälsa oss ifrå våra ovänner, och utur allas deras hand, som hata oss;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 Och bevisa barmhertighet med våra fäder, och minnas på sitt helga Testamente;
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Och på den ed, som han svorit hafver vårom fader Abraham, att gifva oss;
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 Att vi, frälste utur våra ovänners hand, måtte honom tjena utan fruktan;
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 I helighet och rättfärdighet, för honom, i alla våra lifsdagar.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 Och du barn skall kallas dens Högstas Prophet; du skall gå för Herranom, till att bereda hans vägar;
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 Och gifva hans folke salighetenes kunskap, till deras synders förlåtelse;
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 Genom vår Guds innerliga barmhertighet, genom hvilken uppgången af höjdene hafver oss besökt;
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 Till att uppenbaras dem, som sitta i mörkret och dödsens skugga, och styra våra fötter på fridsens väg.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 Och barnet växte upp, och stärktes i Andanom; och vistades i öknene, till den dagen han skulle framkomma för Israels folk.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

< Lukas 1 >