< 3 Mosebok 27 >

1 Och Herren talade med Mose, och sade:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Tala med Israels barn, och säg till dem: Om någor gör Herranom ett besynnerligit löfte, så att han skattar sig;
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Duk sa’ad da mutum ya yi rantsuwa ta musamman zai keɓe wani ga Ubangiji, ta wurin biyan kuɗaɗen fansa,
3 Så skall detta vara skattningen: en mansperson tjuguåra gammal, intill sextio år, skall du skatta på femtio silfversiklar, efter helgedomens sikel;
ga yadda ma’aunin biyan zai kasance, mutum mai shekara tsakanin ashirin da sittin, za a biya azurfa hamsin.
4 En qvinnosperson på tretio siklar.
Mace kuma za a biya azurfa talatin.
5 Men ifrå fem år in till tjugu år, om det är en mansperson, skall du skatta honom på tjugu siklar; en qvinnosperson på tio siklar.
Saurayi mai shekara tsakanin biyar da ashirin, za a biya azurfa ashirin, yarinya kuma azurfa goma.
6 Är det en månad gammalt, intill fem år, om det är en mansperson, skall du skatta det på fem silfversiklar; en qvinno på tre silfversiklar.
Yaro mai shekara tsakanin wata ɗaya da shekara biyar, za a biya azurfa biyar,’yar yarinya kuma azurfa uku.
7 Men är det sextioåra gammalt, och derutöfver, och är en mansperson, skall du skatta honom på femton silfversiklar; en qvinno på tio siklar.
Namijin da ya fi shekara sittin, za a biya azurfa goma sha biyar, mace kuma azurfa goma.
8 Om han är för fattig till sådana skattning, så skall han gå för Presten, och Presten skall skatta honom; och han skall skatta honom efter som hans hand, som löftet gjort hafver, förvärfva kan.
In mai alkawarin matalauci ne da ba zai iya biyan ƙayyadadden abin da aka tsara ba, sai yă tafi wurin firist, shi firist kuma yă duba yadda mutumin da ya yi alkawarin zai iya biya. Sa’an nan mutumin zai biya abin da firist ya faɗa.
9 Om det är af boskap, det man Herranom offra må, allt det man Herranom gifver, det är heligt.
“‘In abin da ya yi alkawarin yardajje ne a matsayin hadaya ga Ubangiji, wannan dabbar da aka bayar ga Ubangiji, za tă zama mai tsarki.
10 Man skall icke vexla det, eller förvandlat, ett godt för ett ondt, eller ett ondt för ett godt. Om någor vexlar det, ett djur för det andra, så skola de båda vara helig.
Kada yă yi musayarta ko yă yi musaya mai kyau da marar kyau, ko marar kyau da mai kyau; in lalle ne yă yi musayar dabbar da wata, to, duk wannan da kuma wanda zai yi musayar da ita za su zama masu tsarki.
11 Är det djuret orent, det man icke bör offra Herranom, så skall man hafva det fram för Presten;
In abin da ya yi alkawari dabba ce marar tsarki, wadda ba yardajje ba ce, a matsayin hadaya ga Ubangiji, dole a kai dabbar wa firist,
12 Och Presten skall skatta det, om det är godt eller ondt. Och det skall blifva vid Prestens skattning.
wanda zai yanke hukunci dacewarta, ko mai kyau ce, ko marar kyau. Duk darajar da firist ya kimanta, haka za tă zama.
13 Vill någor lösa det, han skall gifva femtedelen utöfver skattningena.
In mai shi yana so yă fanshi dabbar, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajarta.
14 Om någor helgar sitt hus, så att det skall vara Herranom heligt, så skall Presten skatta det, om det är godt eller ondt. Och efter som Presten skattar det, så skall det blifva.
“‘In mutum ya miƙa gidansa a matsayin wani abu mai tsarki ga Ubangiji, firist zai daidaita dacewar ko mai kyau ne, ko marar kyau. Duk darajar da firist ya kimanta, haka za tă zama.
15 Men om han, som det helgat hafver, vill det lösa, skall han gifva den femte delen i silfver mer än som det skattadt är, och så skall det varda hans.
In mutumin da ya keɓe gidansa ya fanshe shi, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar, gidan kuma zai zama nasa.
16 Om någor helgar Herranom ett stycke åker af sitt arfvegods, så skall den skattad varda efter som han bär. Bär han en homer korn, så skall han gälla femtio silfversiklar.
“‘In wani ya keɓe wa Ubangiji wani sashe daga cikin gonarsa ta gādo, sai yă kimanta kuɗin gonar daidai da yawan irin da za a iya shuka a gonar. Za a kimanta kuɗin a kan shekel hamsin na irin sha’ir.
17 Men helgar han sin åker straxt ifrå klangåret, så skall han gälla efter hans värde.
In ya keɓe gonarsa a Shekara ta Murna, darajar da aka kimanta za tă zauna.
18 Hafver han helgat honom efter klangåret, så skall Presten räkna honom efter de åren, som tillbakastå intill klangåret, och derefter skatta honom desto ringare.
Amma in ya keɓe gonar bayan Shekara ta Murnan, firist zai kimanta darajar bisa ga yawan shekarun da suka rage har zuwa Shekara ta Murna mai zuwa, sai a rage darajar da aka kimanta a kanta.
19 Vill han, som honom helgat hafver, lösa åkren, så skall han gifva femtedelen i silfver, mer än han skattad är, och så skall han varda hans.
In mutumin da ya keɓe gonar, yana so yă fanshe ta, to, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajarta, gonar kuwa tă zama nasa.
20 Vill han icke lösan, utan säljer honom enom androm, så skall han icke mer lösa honom;
In kuma bai fanshe gonar ba, ko kuwa in ya sayar wa wani dabam, ba za a taɓa fanshe ta ba.
21 Utan den samme åkren, när han i klangåret lös utgår, skall vara helig Herranom, såsom en förspilld åker, och skall vara Prestens arfvegods.
Sa’ad da aka saki gonar a Shekara ta Murna, za tă zama mai tsarki, a matsayin gonar da aka miƙa ga Ubangiji, za tă zama mallakar firistoci.
22 Om någor helgar Herranom en åker, den han köpt hafver, och icke hans arfvegods är;
“‘In mutum ya keɓe gonar da ya saya, wadda take ba sashe na gonar iyali ba, ga Ubangiji,
23 Så skall Presten räkna honom hvad han gälla kan intill klangåret, och han skall på samma dagen gifva den skattningen ut, att hon skall vara Herranom helig.
firist zai kimanta darajarta har Shekara ta Murna, dole kuma mutumin yă biya darajarta a ranar, a matsayin wani abu mai tsarki ga Ubangiji.
24 Men på klangåret skall han komma till honom igen, som honom sålt hade, att han blifver hans arfvegods i landena.
A Shekara ta Murna ɗin, gonar za tă dawo ga mutumin da aka saye ta daga wurinsa, wanda yake mai gonar.
25 All skattning skall ske efter helgedomens sikel; men en sikel gör tjugu gera.
A kimanta kowace daraja bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, gera ashirin ga shekel.
26 Det förstfödda ibland boskapen, det Herranom eljest tillhörer, skall ingen helga, vare sig oxe eller får; ty det är Herrans.
“‘Ba wani da zai iya keɓe ɗan farin dabba, da yake ɗan fari ya riga ya zama na Ubangiji, ko na saniya, ko na tunkiya, na Ubangiji ne.
27 Är något orent på boskapen, så skall man lösa det efter sitt värde, och derutöfver gifva den femte delen. Vill han icke lösa det, så må det säljas efter sitt värde.
In tana cikin dabbobin da suke marasa tsarki, zai iya saye ta a darajar da aka kimanta, yă ƙara da kashi ɗaya bisa biyar na darajarta. In bai fanshe ta ba, sai a sayar da ita a darajar da aka kimanta.
28 Man skall intet spillgifvet sälja eller lösa, det någor Herranom tillspillogifver, af allt det hans ägodelar är, vare sig menniska, boskap, eller arfåker; ty allt spillgifvet är det aldrahelgasta Herranom.
“‘Amma babu abin da mutum ya mallaka, ya kuma keɓe ga Ubangiji, ko mutum ne, ko dabba, ko ganar iyali da za a sayar, ko a fansa; kome da aka keɓe a wannan hanya, mafi tsarki ne ga Ubangiji.
29 Man skall icke lösa någon spillgifven mennisko; utan hon skall döden dö.
“‘Babu wani da aka keɓe don hallaka da za a fansa; dole a kashe shi.
30 All tionde i landet, både af landsens säd, och af frukten af trän, höra Herranom till, och skola vara helig Herranom.
“‘Ushirin kome daga gona, ko hatsi daga ƙasa, ko’ya’yan itatuwa daga itatuwa, na Ubangiji ne, mai tsarki ne ga Ubangiji.
31 Vill någor lösa sin tiond, han skall gifva femtedelen utöfver.
In mutum ya fanshi wani zakansa, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar.
32 Och all tiond af fä och får, och allt det under ris går, det är en helig tiond Herranom,
Ushirin gaba ɗaya na garken shanu, da na tumaki, kowane kashi ɗaya bisa goma na dabbar da ta wuce ƙarƙashin sandan mai kiwo, za tă zama mai tsarki ga Ubangiji.
33 Man skall icke fråga, om det är godt eller ondt; man skall icke heller vexlat. Om någor vexlar det, så skall både vara heligt, och icke löst varda.
Kada kuwa ya zaɓa mai kyau daga marar kyau, ko yă yi musaya. In ya yi musaya kuwa, dabbar da wadda ya musayar, za su zama masu tsarki, ba kuma za a fanshe su ba.’”
34 Desse äro de bud, som Herren böd Mose till Israels barn på Sinai berg.
Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai saboda Isra’ilawa.

< 3 Mosebok 27 >