< Johannes 7 >

1 Derefter vistades Jesus i Galileen; ty han ville icke vistas i Judeen, derföre att Judarna foro efter att dräpa honom.
Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
2 Och var då hardt vid Judarnas löfhyddohögtid.
To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
3 Då sade hans bröder till honom: Gack hädan, och gack in i Judeen, att dine Lärjungar må ock se din verk, som du gör.
Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
4 Ty ingen, som vill uppenbar vara, förhandlar något hemliga; om du det gör, så uppenbara dig för verldene.
Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5 Ty hans bröder trodde icke heller på honom.
Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
6 Då sade Jesus till dem: Min tid är icke än kommen; men edar tid är alltid redo.
Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
7 Verlden kan icke hata eder; men mig hatar hon; ty jag bär vittne om henne, att hennes verk äro ond.
Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8 Går I upp till denna högtidsdagen; jag vill icke ännu gå upp till denna högtiden; ty min tid är icke ännu fullbordad.
Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
9 Då han hade detta sagt till dem, blef han i Galileen.
Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10 Men när hans bröder voro uppgångne, då gick ock han upp till högtiden, dock icke uppenbarliga, utan så hemliga.
Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
11 Då sökte Judarna efter honom i högtidene, och sade: Hvar är han?
Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
12 Och mycket mummel var ibland folket om honom; ty somlige sade: Han är god; och somlige sade: Nej; men han förförer folket.
Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
13 Dock talade ingen uppenbarliga om honom, för Judarnas rädslos skull.
Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14 Då nu half högtiden var öfverstånden, gick Jesus upp i templet, och lärde.
Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
15 Och Judarna förundrade sig, och sade: Huru kan denne Skrift, efter han är icke lärd?
Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
16 Svarade dem Jesus, och sade: Min lärdom är icke min, utan hans som mig sändt hafver,
Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 Hvilken som vill lyda hans vilja, han varder förnimmandes, om denna lärdom är af Gudi, eller om jag talar af mig sjelf.
Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 Hvilken som talar af sig sjelf, han söker sin egen pris; men den som söker hans pris, som honom hafver sändt, han är sannfärdig, och orättfärdighet är icke i honom.
Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 Gaf icke Moses eder lagen? Och likväl gör ingen af eder lagen fullt. Hvi söken I efter att döda mig?
Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 Svarade folket, och sade: Du hafver djefvulen; ho söker efter att döda dig?
Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
21 Svarade Jesus, och sade till dem: Jag gjorde ena gerning, och der undren I alle på.
Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
22 Fördenskull gaf Moses eder omskärelsen; icke, att hon är af Mose, utan af fäderna; och likväl omskären I menniskona om Sabbathen.
Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23 Tager nu menniskan omskärelsen om Sabbathen, på det att Mose lag icke skall varda bruten; på mig blifven I misslynte, att jag gjorde hela menniskona helbregda om Sabbathen?
Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24 Dömer icke efter ansigtet; utan dömer en rätt dom.
Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25 Då sade någre af Jerusalem: Är icke denne, den de fara efter att döda?
Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26 Och si, han talar fritt, och de tala intet till honom. Veta nu vare öfverste förvisso, att han är visst Christus?
Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27 Dock vi vete, hvadan denne är; men när Christus kommer, vet ingen hvadan hanar.
da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28 Då ropade Jesus i templet, lärde, och sade: Ja, I kännen mig, och I veten hvadan jag är; och jag är icke kommen af mig sjelf; utan den mig sändt hafver han är sannfärdig, den I icke kännen.
Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29 Men jag känner honom; ty jag är af honom; och han sände mig.
Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30 Då foro de efter att gripa honom; dock kom ingen sina händer vid honom; ty hans tid var icke än då kommen.
Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
31 Men månge af folket trodde på honom, och sade: När Christus kommer, icke varder han mer tecken görandes, än denne gjort hafver?
Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
32 Så hörde de Phariseer, att folket mumlade sådant om honom; och sände Phariseerna och de öfverste Presterna tjenarena ut, till att gripa honom.
Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33 Då sade Jesus till dem: Jag är ännu en liten tid när eder; och så går jag bort till honom, som mig sändt hafver.
Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
34 I skolen söka mig, och intet finna mig; och der jag är, dit kunnen I icke komma.
Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
35 Då sade Judarna emellan sig: Hvart vill denne gå, att vi skole icke finna honom? Månn han vilja gå ut ibland Hedningarna, som här och der förströdde äro, och lära Hedningarna?
Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
36 Hvad är det för ett tal, som han sade: I skolen söka mig, och intet finna mig; och der jag är, dit kunnen I icke komma?
Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
37 Men på yttersta dagen i högtidene, den ock störst var, stod Jesus, och ropade, sägandes: Hvilken som törster, han komme till mig, och dricke.
To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
38 Hvilken som tror på mig, såsom Skriften säger, af hans qved skola flyta lefvandes vattens strömmar.
Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
39 Men det sade han om Andan, hvilken de få skulle, som på honom trodde; ty den Helge Ande var icke än då på färde; ty Jesus var icke ännu förklarad.
Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40 Då nu månge af folket hörde detta talet, sade de: Denne är sannerliga en Prophet.
Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 En part sade: Denne är Christus. Men somlige sade: Icke skall Christus komma af Galileen?
Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
42 Säger icke Skriften, att Christus skall komma af Davids säd, och af den staden BethLehem, der David var?
Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 Och vardt en tvedrägt ibland folket för hans skull.
Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 Och somlige af dem ville gripa honom; men ingen kom händer vid honom.
Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 Då kommo tjenarena till öfversta Presterna och Phariseerna; och de sade till dem: Hvi hafven I icke haft honom hit?
Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 Tjenarena svarade: Aldrig hafver någor menniska så talat som denne mannen.
Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 Svarade dem Phariseerna: Ären I icke ock förförde?
Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 Icke hafver någor af öfverstarna, eller Phariseerna, trott på honom?
Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 Utan detta folket, som icke vet lagen, är förbannadt.
Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 Då sade till dem Nicodemus, den som kom till honom om nattena, hvilken var en af dem:
Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 Icke dömer vår lag någon mennisko, med mindre man först förhörer honom, och får veta hvad han gör?
“Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
52 Svarade de, och sade till honom: Äst du icke ock en Galilee? Ransaka, och se, att af Galileen är ingen Prophet uppkommen.
Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
53 Och så gick hvar och en hem till sitt.
Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.

< Johannes 7 >