< Johannes 5 >

1 Derefter var en Judarnas högtid; och Jesus for upp till Jerusalem.
Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima.
2 Men i Jerusalem är en dam, vid fårahuset, som het på Ebreisko Bethesda, och hade fem skjul;
To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar.
3 Deruti lågo en stor hop sjuke, blinde halte, borttvinade, och bidde efter att vattnet skulle röras.
Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin [suna jira a dama ruwan].
4 Ty en Ängel steg ned i dammen, på en viss tid, och rörde vattnet; den der nu först steg ned i vattnet, sedan det var rördt, han blef helbregda, ehvad sjukdom han hade.
Gama mala'ikan Ubangiji kan sabko a cikin tabkin ya dama ruwan, wanda ya fara taba ruwan sai ya warke komai cutar da yake da ita.
5 Så var der en man, som hade varit sjuk i åtta och tretio år.
Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas.
6 Då Jesus fick se honom der han låg, och förnam att han nu i lång tid hade legat sjuk, sade han till honom: Vill du blifva helbregda?
Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, “Ko kana so ka warke?”
7 Svarade den sjuke honom: Herre, jag hafver ingen, som hafver mig i dammen, när vattnet är rördt; men förr än jag kommer, då är en annar stigen in för mig.
Sai mai rashin lafiyar ya amsa ya ce, “Malam, bani da kowa da zai sa ni a cikin tabkin idan ruwan ya motsa. Yayinda na ke kokari sai wani ya riga ni.”
8 Då sade Jesus till honom: Statt upp, tag din säng, och gack.
Yesu ya ce masa,” Ka tashi ka dauki shimfidarka ka tafi.”
9 Och straxt blef den mannen helbregda, och tog sin säng, och gick; och det var på en Sabbathsdag.
Nan dan nan Mutumin ya warke, ya dauki shimfidarsa ya tafi. Ranar kuwa Asabar ce.
10 Då sade Judarna till honom, som var vorden helbregda: Det är Sabbath; dig är icke lofligit bära sängena.
Sai Yahudawa suka ce da wanda aka warkar din, “Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka dauki shimfidarka ba.”
11 Svarade han dem: Den som gjorde mig helbregda, han sade till mig: Tag din säng, och gack.
Sai ya amsa ya ce, “Ai wanda ya warkar da ni, shine ya ce mani 'Dauki shimfidarka, ka tafi.”
12 Då sporde de honom: Ho är den mannen, som dig sade: Tag din säng, och gack?
Suka tambaye shi, “wane mutum ne ya ce maka, 'Dauki shimfidar ka yi tafiya'?”
13 Men han, som helbregda var vorden, visste icke, ho han var; ty Jesus var undanviken, efter mycket folk var i det rummet.
Sai dai, shi wanda aka warka din, ba san ko wanene ya warkar da shi ba, domin Yesu ya riga ya tafi aboye, saboda akwai taro a wurin.
14 Derefter fann Jesus honom i templet, och sade till honom: Si, du äst vorden helbregda; synda icke härefter, att dig icke vederfars något värre.
Bayan haka, Yesu ya same shi a Haikalin, ya ce masa, “ka ga fa, ka warke. To, kada ka kara yin zunubi don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka.”
15 Då gick den mannen bort, och sade Judomen, att Jesus var den, som honom hade helbregda gjort;
Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahuduwa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
16 Och derföre förföljde Judarna Jesum, och sökte efter att döda honom, efter han detta gjorde på Sabbathen.
To saboda haka Yahudawa suka fara tsanantawa Yesu, don ya yi wadannan abubuwa ran Asabar.
17 Då svarade Jesus dem: Min Fader verkar intill nu; och jag verkar ock.
Yesu kuwa ya amsa masu ya ce, “Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina aiki.”
18 Derföre sökte Judarna ändå mer efter att döda honom; ty han ej allenast bröt Sabbathen, utan ock sade Gud vara sin Fader, görandes sig sjelf lik med Gud.
Saboda haka, Yahudawa suka kara nema su kashe shi ba don ya keta Asabar kadai ba, amma kuma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato yana maida kansa dai-dai da Allah.
19 Då svarade Jesus, och sade till dem: Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Sonen kan intet göra af sig sjelf, utan det han ser Fadren göra; ty allt det han gör, det gör ock Sonen.
Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi.
20 Ty Fadren älskar Sonen, och visar honom allt det han gör; och varder än visandes honom större verk än dessa äro, att I skolen undra derpå.
Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.
21 Ty såsom Fadren uppväcker de döda, och gör dem lefvande; så gör ock Sonen lefvande hvem han vill.
Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa.
22 Ty icke dömer heller Fadren någon; utan hafver all dom gifvit Sonenom;
Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan,
23 På det alle skola hedra Sonen, såsom de hedra Fadren. Hvilken som icke hedrar Sonen, han hedrar icke Fadren, som honom sändt hafver.
domin kowa ya girmama Dan, kamar yadda suke girmama Uban. Shi wanda ba ya girmama Dan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi.
24 Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Hvilken som hörer mitt tal, och tror honom, som mig sändt hafver, han hafver evinnerligit lif, och kommer icke i domen; utan är gången ifrå döden till lifvet. (aiōnios g166)
Hakika, hakika, duk mai jin Maganata, yana kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami ba kuma za a kashe shi ba, domin ya ratse daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
25 Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Den tid skall komma, och är nu allaredo, att de döde skola höra Guds Sons röst; och de henne höra, de skola lefva.
Hakika hakika, ina gaya maku, lokaci na zuwa, har ma ya yi da matattatu za su ji muryar Dan Allah, wadanda suka ji kuwa za su rayu.
26 Ty såsom Fadren hafver lif i sig sjelfvom, så hafver han ock gifvit Sonenom hafva lif i sig sjelfvom;
Kammar yada Uba ya ke da rai a cikinsa, haka ya ba Dan don ya zama da rai cikin kansa.
27 Och hafver desslikes gifvit honom magt att döma; derföre, att han menniskones Son är.
Uban ya kuma ba Dan ikon zartar da hukunci, saboda shi ne Dan Mutum.
28 Förundrer eder icke öfver detta: ty den stund skall komma, i hvilko alle de i grifterna äro, skola höra hans röst.
Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk wadanda suke kaburbura za su ji muryarsa,
29 Och de som väl hafva gjort, skola framgå till lifsens uppståndelse; men de som illa hafva gjort, till domsens uppståndelse.
su kuma fito: wadanda suka aikata nagarta zawa tashi na rai, wadanda suka aikata mugunta kuwa zuwa tashi na hukunci.
30 Intet kan jag göra af mig sjelf. Som jag hörer, så dömer jag, och min dom är rätt; ty jag söker icke min vilja, utan Fadrens vilja, som mig sändt hafver.
Ba na iya yin kome ni da kai na. Yadda na ke ji, haka nake yin hukunci, Hukunci na kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
31 Om jag vittnar om mig sjelf, då är mitt vittnesbörd icke sant.
Idan zan yi shaida game da kaina, shaidata baza ta zama gaskiya ba.
32 En annar är, som vittnar om mig; och jag vet, att det vittnesbörd sant är, som han vittnar om mig.
Akwai wani wanda ya ke bada shaida game da ni, na kuwa sani shaidar da yake bayarwa game da ni gaskiya ce.
33 I sänden till Johannes, och han gaf vittnesbörd till sanningen;
Kun aika zuwa wurin Yahaya, shi kuma ya yi shaidar gaskiya.
34 Men jag tager intet vittnesbörd af mennisko; utan säger detta, på det I skolen varda salige.
Duk da haka shaidar da na karba bata mutum bace. Na fadi wadanan abubuwa domin ku sami ceto.
35 Han var ett brinnande och skinande ljus; och I villen en tid långt fröjdas i hans ljus.
Yahaya fitila ne mai ci, mai haske ne kuma, kun yarda ku yi farinciki da haskensa dan lokaci kadan.
36 Men jag hafver ett större vittnesbörd än Johannis vittnesbörd; ty de verk, som Fadren hafver gifvit mig att jag skall fullborda, de samma verk, som jag gör, vittna om mig, att Fadren hafver sändt mig.
Amma shaidar da ni ke da ita ta fi ta Yahaya karfi. Domin ayyukan da Uba ya bani ni in yi, wato ainihin ayyukan da nake yi, su ne suke shaida ta cewa, Uba ne ya aiko ni.
37 Och Fadren, som mig sände, han hafver vittnat om mig: I hafven hvarken någon tid hört hans röst, eller sett hans skepelse;
Uba wanda ya aiko ni, shi da kansa ya shaide ni. Ba ku taba jin muryar sa ba, ko ganin kamanninsa.
38 Och hans ord hafven I icke blifvandes i eder; ty I tron icke honom, som han sändt hafver.
Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39 Ransaker Skrifterna; ty I menen eder hafva evinnerligit lif i dem; och de äro de som vittna om mig. (aiōnios g166)
Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. (aiōnios g166)
40 Och I viljen icke komma till mig, att I måtten få lif.
kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
41 Jag tager ingen pris af menniskor.
Ba na karbar yabo daga wurin mutane,
42 Men jag känner eder, att I icke hafven Guds kärlek uti eder.
amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
43 Jag är kommen i mins Faders Namn, och I anammen mig icke; kommer en annar i sitt eget namn, den varden I anammande.
Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi.
44 Huru kunnen I tro, I som tagen pris hvar af androm; och den pris, som kommer allena af Gudi, söken I intet.
Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
45 I skolen icke mena, att jag skall anklaga eder för Fadren; det är en, som eder anklagar, nämliga Moses, den I hoppens uppå.
Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa.
46 Haden I trott Mosi, så haden I ock trott mig; ty om mig hafver han skrifvit.
Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni.
47 Men tron I icke hans skrifter, huru skolen I då tro min ord?
Idan kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?”

< Johannes 5 >