< Johannes 12 >
1 Sex dagar för Påska kom Jesus till Bethanien, der Lazarus hade varit död, den han uppväckte ifrå de döda.
Kwana shida kafin Bikin Ƙetarewa, sai Yesu ya iso Betani, inda Lazarus yake, wanda Yesu ya tā da daga matattu.
2 Der gjorde de honom en nattvard; och Martha tjente, men Lazarus var en af dem som med honom vid bord såto.
A nan aka shirya abincin yamma don girmama Yesu. Marta ta ce yi hidima, Lazarus kuma yana ɗaya cikin waɗanda suke ci tare shi.
3 Då tog Maria ett pund smörjelse, af kosteligit oförfalskadt nardus, och smorde Jesu fötter, och torkade hans fötter med sitt hår; och huset uppfylldes med lukt af smörjelsen.
Sai Maryamu ta ɗauki wajen awo guda na nardi zalla, turare mai tsada; ta zuba a ƙafafun Yesu ta kuma goge ƙafafunsa da gashinta. Gidan duk ya cika da ƙanshin turaren.
4 Då sade en af hans Lärjungar, Judas Simons Ischarioth, som honom förråda skulle:
Amma ɗaya daga cikin almajiransa, Yahuda Iskariyot, wanda daga baya zai bashe shi, bai amince ba ya ce,
5 Hvi vardt icke denna smörjelsen såld för trehundrade penningar, och gifvet fattigom?
“Don me ba a sayar da turaren nan aka kuma ba da kuɗin ga matalauta ba? Ai, kuɗin ya kai albashin shekara guda.”
6 Det sade han, icke att honom vårdade något om de fattiga; utan förty han var en tjuf, och hade pungen, och bar det gifvet vardt.
Ya yi wannan magana ba don ya kula da matalauta ba ne, sai dai don shi ɓarawo ne. Da yake shi ne mai ajiya jakar kuɗin, yakan taimaki kansa da abin da aka sa a ciki.
7 Då sade Jesus: Låt henne blifva; hon hafver det bevarat till mins begrafvelses dag,
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta, an nufa ta ajiye wannan turaren don ranar jana’izata.
8 Ty I hafven alltid fattiga när eder; men mig hafven I icke alltid.
Kullum za ku kasance da matalauta, amma ba kullum za ku kasance tare da ni ba.”
9 Så förnam mycket folk af Judarna, att han var der; och kommo dit, icke allenast för Jesu skull, utan ock att de skulle se Lazarum, den han uppväckt hade ifrå de döda.
Ana cikin haka sai babban taron Yahudawa suka sami labari Yesu yana can suka kuwa zo, ba kawai don shi ba amma don su kuma ga Lazarus, wanda ya tā da daga matattu.
10 Då rådslogo de öfverste Presterna, att de ock skulle dräpa Lazarum;
Saboda haka manyan firistoci suka ƙulla su kashe Lazarus shi ma,
11 Ty månge af Judarna gingo bort för hans skull, och trodde på Jesum.
gama dalilinsa Yahudawa da yawa suna komawa ga Yesu suna kuma ba da gaskiya gare shi.
12 Dagen derefter, när folket, som då mycket kommet var till högtidsdagen, hörde att Jesus kom till Jerusalem;
Kashegari babban taron da suka zo Bikin suka sami labari cewa Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima.
13 Togo de palmqvistar, och gingo ut emot honom, och ropade: Hosianna! Välsignad han, som kommer i Herrans Namn, Israels Konung.
Sai suka ɗaɗɗauko rassan dabino suka fiffita taryensa, suna ɗaga murya suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Mai albarka ne Sarkin Isra’ila!”
14 Och fick Jesus ena åsninno, och satte sig deruppå; såsom skrifvet är:
Yesu ya sami ɗan jaki, ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa,
15 Räds icke, du dotter Zion; si, din Konung kommer, sittandes på en åsninnos fåla.
“Kada ki ji tsoro, ya Diyar Sihiyona; duba, ga sarkinki yana zuwa, zaune a kan aholaki jaki.”
16 Detta förstodo hans Lärjungar icke med det första; utan då Jesus var förklarad, kommo de ihåg, att detta var skrifvet om honom, och att de hade detta gjort honom.
Da fari almajiransa ba su gane dukan wannan ba. Sai bayan da aka ɗaukaka Yesu, sa’an nan suka gane cewa an rubuta waɗannan abubuwa game da shi ne, har ma suka yi masa waɗannan abubuwa.
17 Vittnade ock folket om honom, som med honom varit hade, när han kallade Lazarum utaf grafvene, och väckte honom upp ifrå de döda.
Taron da suke tare da shi a sa’ad da ya kira Lazarus daga kabari ya kuma tā da shi daga matattu suka yi ta baza labarin.
18 Fördenskull kom ock folket emot honom, att de hörde, han hade gjort det tecknet.
Mutane da yawa kuwa suka fita taryensa, saboda sun ji labarin abin banmamakin da ya yi.
19 Då sade Phariseerna emellan sig: I sen, att I intet kunnen skaffa; si, hela verlden löper efter honom.
Saboda haka Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba, wannan ba ya kai mu ko’ina. Ga shi, duk duniya tana bin sa!”
20 Voro ock någre Greker, af dem som uppfarne voro, att tillbedja i högtidene;
To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
21 De gingo till Philippum, som var af Bethsaida i Galileen, och bådo honom, sägande: Herre, vi vilje se Jesum.
Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
22 Philippus kom, och sade det för Andreas; Andreas och Philippus sade det åter till Jesum.
Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.
23 Jesus svarade dem, sägandes: Tiden är kommen, att menniskones Son skall varda förklarad.
Yesu ya amsa ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum.
24 Sannerliga, sannerliga säger jag eder: Utan hvetekornet, som faller i jordena, varder dödt, så blifver det allena; men varder det dödt, så bär det mycken frukt.
Gaskiya nake gaya muku, sai ƙwayar alkama ta fāɗi ƙasa ta mutu, in ba haka ba za tă kasance ƙwaya ɗaya tak. Amma in ta mutu, za tă ba da’ya’ya da yawa.
25 Hvilken som älskar sitt lif, han skall mista det; och hvilken som hatar sitt lif i denna verldene, han skall behålla det till evinnerligit lif. (aiōnios )
Duk mai ƙaunar ransa, zai rasa shi, duk mai ƙin ransa a wannan duniya, zai kiyaye shi har yă zuwa rai madawwami. (aiōnios )
26 Den mig tjenar, han följe mig; och hvar jag är, der skall ock min tjenare vara. Hvilken mig tjenar, honom skall min Fader ära.
Duk wanda zai bauta mini dole yă bi ni, inda kuma nake, a can bawana zai kasance. Ubana zai girmama wanda yake bauta mini.
27 Nu är min själ bedröfvad; och hvad skall jag säga? Fader, hjelp mig utu denna stundene. Dock är jag fördenskull kommen till denna stundena.
“Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
28 Fader, förklara ditt Namn. Då kom en röst af himmelen, och sade: Jag hafver det förklarat, och skall ännu förklarat.
Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
29 Folket, som stod och hörde det, sade: Det var en tordön. Somlige sade: En Ängel talade med honom.
Taron da suke a wurin suka ji, suka ce an yi tsawa; waɗansu kuwa suka ce mala’ika ne ya yi masa magana.
30 Svarade Jesus, och sade: Denna rösten kom icke för mina skull, utan för edra skull.
Yesu ya ce, “An yi wannan muryar saboda amfaninku ne, ba don nawa ba.
31 Nu går domen öfver denna verldena; nu skall denna verldenes Förste utkastas.
Yanzu ne za a yi wa duniyan nan shari’a, yanzu ne za a tumɓuke mai mulkin duniyan nan.
32 Och om jag varder upphöjd ifrå jordene, skall jag draga alla till mig.
Amma ni, sa’ad da aka ɗaga ni daga ƙasa, zan ja dukan mutane gare ni.”
33 Men det sade han, till att beteckna med hvad död han dö skulle.
Ya faɗa haka ne don yă nuna irin mutuwar da zai yi.
34 Svarade honom folket: Vi hafva hört af lagen, att Christus blifver evinnerliga; huru säger då du, menniskones Son måste upphöjas? Ho är denne menniskones Son? (aiōn )
Sai taron suka ce, “Ahab, Dokarmu ta gaya mana cewa, Kiristi zai kasance har abada, to, yaya za ka ce, ‘Dole ne a ɗaga Ɗan Mutum?’ Wane ne wannan ‘Ɗan Mutum’?” (aiōn )
35 Då sade Jesus till dem: Än är Ljuset med eder till en kort tid; vandrer medan I hafven Ljuset, att mörkret begriper eder icke. Hvilken som vandrar i mörkret, han vet icke hvart han går.
Sai Yesu ya ce musu, “Haske zai kasance da ku na ɗan lokaci. Ku yi tafiya yayinda hasken yana nan tare da ku, kada duhu yă cim muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda za shi ba.
36 Medan I hafven Ljuset, tror på Ljuset, att I mågen blifva Ljusens barn. Detta sade Jesus; och gick bort, och dolde sig för dem.
Ku dogara ga hasken yayinda kuke da shi, don ku zama’ya’yan haske.” Da Yesu ya gama magana, sai ya tafi ya ɓuya daga gare su.
37 Och ändock han gjorde så mång tecken för dem, likväl trodde de intet på honom;
Ko bayan Yesu ya yi dukan waɗannan abubuwan banmamaki a gabansu, duk da haka ba su gaskata da shi ba.
38 Att det talet skulle fullkomnas, som Esaias Propheten sagt hade: Herre, ho tror vår predikan; och hvem är Herrans arm uppenbarad?
Wannan ya faru ne, don a cika maganar annabi Ishaya cewa, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu, ga wa kuma aka bayyana hannun ikon Ubangiji?”
39 Derföre kunde de icke tro; ty Esaias hafver åter sagt:
Saboda haka ba su iya gaskatawa ba, domin, kamar yadda Ishaya ya faɗa a wani wuri cewa,
40 Han hafver förblindat deras ögon, och förhärdat deras hjerta; att de icke skola se med ögonen, och icke förstå med hjertat, och omvända sig, att jag måtte hela dem.
“Ya makantar da idanunsu ya kuma taurare zukatansu, don kada su gani da idanunsu, ko su fahimta a zukatansu, ko kuwa su juyo, har in warkar da su.”
41 Detta sade Esaias, när han såg hans härlighet, och talade om honom.
Ishaya ya faɗi haka ne, saboda ya hangi ɗaukakar Yesu, ya kuwa yi magana a kansa.
42 Dock likväl trodde ock månge af de öfversta på honom; men de bekände det icke, för de Phariseers skull, att de icke skulle utkastas af Synagogon.
Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi. Amma saboda Farisiyawa ba su furta bangaskiyarsu ba, don tsoron kada a kore su daga majami’a;
43 Ty de höllo mer af menniskors pris, än af Guds pris.
gama sun fi son yabon mutane, fiye da yabon Allah.
44 Då ropade Jesus, och sade: Den som tror på mig, han tror icke på mig, utan på honom som mig sändt hafver.
Sa’an nan Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Duk wanda ya gaskata da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni ne.
45 Och den mig ser, han ser honom som mig sändt hafver.
Duk mai dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne.
46 Jag är kommen i verldena för ett Ljus, att hvar och en, som tror på mig, skall icke blifva i mörkret.
Na zo cikin duniya a kan ni haske ne, don duk wanda ya gaskata da ni, kada yă zauna a cikin duhu.
47 Och hvilken som hörer min ord, och icke tror, icke dömer jag honom; ty jag är icke kommen till att döma verldena; utan att jag skall frälsa verldena.
“Duk mai jin kalmomina bai kuwa kiyaye su ba, ba ni ba ne nake shari’anta shi. Gama ban zo domin in yi wa duniya shari’a ba, sai dai domin in cece ta.
48 Hvilken mig föraktar, och tager icke min ord, han hafver den honom döma skall; det talet, jag talat hafver, skall döma honom på yttersta dagen.
Akwai mai hukunci saboda wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi kalmomina ba; wannan maganar da na faɗa ita ce za tă hukunta shi a rana ta ƙarshe.
49 Ty jag hafver icke talat af mig sjelf; utan Fadren, som mig sändt hafver, han hafver budit mig hvad jag skall säga, och hvad jag skall tala.
Gama ba don kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ne ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa da kuma yadda zan faɗe shi.
50 Och jag vet, att hans bud är evinnerligit lif; derföre, hvad jag talar, det talar jag såsom Fadren hafver sagt mig. (aiōnios )
Na san cewa umarninsa yana kai ga rai madawwami. Saboda haka duk abin da na faɗa na faɗe shi ne kamar dai yadda Uba ya ce in faɗa.” (aiōnios )