< Joel 2 >

1 Blåser med basuner i Zion, roper på mino helgo berge, darrer, alle landsens inbyggare; ty Herrans dag kommer, och är hardt när;
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 En mörk dag, en bister dag, en mulen dag, och dimbog dag, lika som morgonrodnen utbreder sig öfver bergen; nämliga ett stort och mägtigt folk; hvilkets like tillförene icke varit hafver, och härefter icke varda skall i evig tid.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 För honom går en förtärande eld, och efter honom en brinnande låge; landet är för honom lika som en lustgård; men efter honom lika som en vild öken, och ingen skall undslippa honom.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 De äro till seende såsom hästar, och ränna såsom resenärer.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 De springa ofvanpå bergen, lika som der vagnar bullrade, och såsom en låge dånar i halm, såsom ett mägtigt folk, som till strids rustadt är.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Folken skola förskräcka sig för honom; all ansigte äro så blek som lerpottor.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 De skola löpa såsom hjeltar, och bestiga murarna såsom krigsmän; hvar och en skall draga rätt fram, och intet försumma sig.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 Ingen skall hindra den andra, utan hvar och en skall gå i sin orden; och när de storma och infalla, skola de intet såre varda.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 De skola rida omkring i stadenom, löpa på murarna, och stiga in uti husen; och såsom en tjuf infalla genom fenstren.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 För honom darrar landet, och himmelen bäfvar; sol och måne varda mörk, och stjernorna förhålla sitt sken;
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 Ty Herren skall låta gå sin dunder för sinom här; ty hans här är ganska stor och mägtig; han skall uträtta hans befallning; ty Herrans dag är stor, och fast förskräckelig; ho kan lida honom?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Så säger nu Herren: Vänder eder till mig af allt hjerta, med fastande, med gråtande, och med sörjande.
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 Rifver edor hjerta, och icke edor kläder, och vänder eder till Herran, edar Gud; ty han är nådelig, barmhertig, tålig, och af stor mildhet, och låter sig snart ångra straffet.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Ho vet, han förbarmar sig ju ännu och efter sitt straff nåde beviser, till spisoffer och drickoffer Herranom edrom Gudi.
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blåser med basun i Zion; helger ena fasto; kaller menigheten tillhopa.
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Församler folket, helger församlingena; sammankaller de äldsta, hafver de unga barn och däggobarn tillsammans; brudgummen gånge utu sinom kammar, och bruden utu sitt mak.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Låter Presterna, Herrans tjenare, gråta emellan förhuset och altaret, och säga: Herre, skona dino folke, och låt icke din arfvedel till skam varda, så att Hedningarna få råda öfver dem; hvi vill du låta säga ibland folken: Hvar är nu deras Gud?
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 Så skall då Herren hafva nit om sitt land, och skona sino folke.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 Och Herren skall svara, och säga till sitt folk: Si, jag skall sända eder korn, must och oljo tillfyllest, så att I skolen deraf nog hafva; och skall icke mer låta eder på skam komma ibland Hedningarna.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 Och skall jaga dem af nordan långt bort ifrån eder, och drifva honom bort uti ett torrt och öde land; nämliga hans ansigte bort emot hafvet österut, och hans ända bort emot yttersta hafvet; han skall ruttna och lukta för sina högfärds skull.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Frukta dig intet, du land, utan gläd dig, och var vid ett godt mod; ty Herren kan ock göra mägtig ting.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Frukter eder intet, I djur på markene; ty boningarna i öknene skola grönskas, och trän bära sin frukt, och fikonaträn och vinträn skola väl bära.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 Och I Zions barn, fröjder eder, och varer glade i Herranom, edrom Gud, den eder nådeligit regn gifver, och sänder eder neder morgonregn och aftonregn, såsom tillförene;
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 Att ladorna varda fulla med korn, och presserna öfverflödighet af must och oljo hafva skola.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 Och jag skall gifva eder de åren igen, som gräshoppor, flogmatkar, lus och gräsmatkar, som min stora här voro, den jag ibland eder sände, uppätit hafva;
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 Att I skolen hafva nog till att äta, och prisa Herrans edars Guds Namn, den ibland eder under gjort hafver; och mitt folk skall icke mer till skam varda.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 Och I skolen förnimma, att jag är midt ibland Israel, och att jag är Herren, edar Gud, och ingen mer; och mitt folk skall icke mer till skam varda.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 Och derefter skall jag utgjuta min Anda öfver allt kött, och edra söner och döttrar skola prophetera; edre äldste skola hafva drömmar, och edre ynglingar skola se syner.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Och vill jag på den tiden utgjuta min Anda, både öfver tjenare och tjenarinnor;
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 Och skall gifva undertecken i himmelen och på jordene, nämliga blod, eld och rökdamb.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 Solen skall förvandlad varda uti mörker, och månen uti blod, förr än den store och förskräckelige Herrans dag kommer.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 Och det skall ske: Ho som helst Herrans Namn åkallandes varder, han skall frälst varda; ty på Zions berg och i Jerusalem skall en salighet vara, såsom Herren sagt hafver, och när de andra qvarblefna, de Herren kallandes varder.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joel 2 >