< Job 9 >
2 Ja, jag vet det fullväl, att så är, att en menniska icke kan bestå rättfärdig för Gud.
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Täckes honom träta med honom, så kan han icke svara honom ett emot tusende.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Han är vis och mägtig; hvem hafver det dock gått väl af, som sig hafver satt emot honom?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Han försätter bergen, förr än de det förnimma; hvilka han i sine vrede omkastar.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Han rörer jordena af sitt rum, så att hennes pelare bäfva.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Han talar till solena, så går hon intet upp, och han förseglar stjernorna.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Han allena utsträcker himmelen, och går på hafsens vägar.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Han gör Karlavagnen ( på himmelen ) och Orion; sjustjernorna, och de stjernor söderut.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Han gör mägtig ting, som man icke utransaka kan, och under, deruppå intet tal är.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Si, han går framom mig, förr än jag varder det varse; och han förvandlar sig, förr än jag det märker.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Si, om han går hasteliga bort, ho vill hemta honom igen? Ho vill säga till honom: Hvad gör du?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Han är Gud, hans vrede kan ingen stilla; under honom måste buga sig de stolta herrar.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Huru skulle jag då svara honom, och finna några ord emot honom?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Om jag än rätt hafver, så kan jag dock likväl intet svara honom; utan måste i rättenom bedjas före.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Och om jag än åkallade honom, och han hörde mig; så tror jag dock icke, att han hörer mina röst.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Ty han far öfver mig med storm, och gör mig såren mång utan sak.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 Han låter icke min anda vederqvickas, utan gör mig full med bedröfvelse.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Vill man magt, så är han för mägtig; vill man rätten, ho vill vittna med mig?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Om jag säger att jag är rättfärdig, så fördömer han mig dock; är jag from, så för han mig dock till ondan.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Är jag än from, så tör min själ dock intet hålla sig dervid; jag begärer intet mer lefva.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Det är det som jag sagt hafver; han förgör både den goda, och den ogudaktiga.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 När han begynner till att slå, så dräper han straxt, och begabbar de oskyldigas frestelse.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Men landet varder gifvet under dens ogudaktigas hand, att han undertrycker dess domare; är det icke så, huru skulle det annars vara.
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Mine dagar hafva varit snarare än en löpare; de hafva flytt, och hafva intet godt sett.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 De äro förgångne såsom stark skepp; såsom en örn flyger till maten.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 När jag tänker: Jag vill glömma bort min klagan; jag vill förvandla mitt ansigte, och vederqvicka mig;
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 Så fruktar jag mig för all min sveda, vetandes, att du icke låter mig vara oskyldig.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Är jag nu ogudaktig, hvi hafver jag då sådana onyttiga vedermödo?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Om jag än tvådde mig i snö, och gjorde mina händer rena i källo;
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Så doppar du mig dock i träck, och min kläder varda mig illa ståndande.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Ty han är icke min like, dem jag svara kunde, att vi måtte både komma för rätten.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Det är ingen, som oss åtskiljer; som sätter sina hand emellan oss båda.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Han tage sitt ris ifrå mig, och låte sin förskräckelse komma ifrå mig;
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 Att jag må tala, och icke mer torf frukta för honom; ty jag vet mig oskyldig.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.