< Job 22 >

1 Då svarade Eliphas af Thema, och sade:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Menar du att en man kan liknas vid Gud; eller någor är så klok, att han kan likna sig vid honom?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Menar du att dem Allsmägtiga behagar, att du räknar dig så from? Eller hvad hjelper det honom, om än dine vägar utan brist voro?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Menar du han fruktar att straffa dig, och gå till rätta med dig?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Ja, din ondska är fast stor, och uppå din orättfärdighet är ingen ände.
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Du hafver tagit af dinom broder pant utan sak; du hafver dragit kläden af dem nakna.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Du hafver icke gifvit dem trötta vatten dricka; du hafver nekat dem hungroga ditt bröd.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 Du hafver brukat våld i landena, och bott deruti med stort prål.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Enkor hafver du låtit gå ohulpna, och sönderbrutit de faderlösas armar.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Derföre äst du omvefvad med snaro, och fruktan hafver dig hasteliga förskräckt.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 Skulle du då icke se mörkret, och vattufloden icke öfvertäcka dig?
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Si, Gud är hög i himmelen, och ser stjernorna uppe i höjdene;
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Och du säger: Hvad vet Gud? Skulle han kunna döma det i mörkret är?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Skyn skyler för honom, och han ser intet; han vandrar i himmelens omgång.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Vill du akta på verldenes lopp, der de orättfärdige uti gångne äro?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Hvilke förgångne äro, förr än tid var, och vattnet hafver bortsköljt deras grund;
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 De som till Gud sade: Far ifrån oss; hvad skulle den Allsmägtige kunna göra dem?
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Ändock han uppfyllde deras hus med ägodelar; men de ogudaktigas råd vare långt ifrå mig.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 De rättfärdige skola få det se, och glädja sig; och den oskyldige skall bespotta dem.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Deras väsende skall försvinna, och det qvart är af dem, skall elden förtära.
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Så förlika dig nu med honom, och haf frid; derutaf skall du hafva mycket godt.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Hör lagen utaf hans mun, och fatta hans tal uti ditt hjerta.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Om du omvänder dig till den Allsmägtiga, så skall du uppbyggd varda; och kasta det orätt är långt ifrå dine hyddo;
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 Så skall han gifva guld igen för stoft, och för sten gyldene bäcker.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 Och du skall hafva guld nog, och silfver skall dig med hopom tillfalla.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Då skall du hafva din lust i dem Allsmägtiga, och upplyfta ditt anlete till Gud.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Du skall bedja honom, och han skall höra dig; och ditt löfte skall du betala.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Ehvad du tager dig före, det skall han låta dig väl af gå; och ljus skall skina på dina vägar.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Förty de som sig ödmjuka, dem upphöjer han; och den som sin ögon nederslår, han skall blifva frälst;
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Och den oskyldige skall hulpen varda; för sina händers renhets skull skall han hulpen varda.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >