< Jeremia 29 >

1 Detta äro de ord, i de brefvena, som Propheten Jeremia sände af Jerusalem, till de igenlefda äldsta som bortförde voro, och till Presterna, och Propheterna, och till allt folket, som NebucadNezar ifrå Jerusalem till Babel bortfört hade;
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 Sedan Konung Jechonia och Drottningen, med kamererarena, och Förstarna i Juda och Jerusalem, samt med timbermän och smeder i Jerusalem, borto voro;
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 Genom Elasa, Saphans son, och Gemaria, Hilkia son, hvilka Zedekia, Juda Konung, sände till Babel, till NebucadNezar, Konungen i Babel, och sade:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 Detta säger Herren Zebaoth, Israels Gud, till alla fångar, som jag hafver låtit bortföra ifrå Jerusalem till Babel:
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Bygger hus, der I uti bo kunnen; planterer trädgårdar, der I frukt af äta mågen.
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Tager eder hustrur, och föder söner och döttrar; gifver edra söner hustrur, och gifver edra döttrar män, att de måga föda söner och döttrar; föröker eder der, så att I icke ären få.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Söker stadsens bästa, dit jag hafver låtit bortföra eder, och beder för honom till Herran; ty då honom väl går, så går eder ock väl.
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 Ty detta, säger Herren Zebaoth, Israels Gud: Låter icke de Propheter, som när eder äro, och de spåmän bedraga eder, och sköter intet edra drömmar som I drömmen;
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 Ty de spå eder lögn i mitt Namn; jag hafver intet sändt dem, säger Herren.
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 Ty så säger Herren; När i Babel sjutio år ute äro, så skall jag besöka eder, och skall uppväcka mitt nådeliga ord öfver eder, att jag skall låta eder komma till detta rum igen.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 Ty jag vet väl, hvad tankar jag hafver om eder, säger Herren, nämliga fridsens tankar, och icke bedröfvelsens, att jag skall gifva eder den ända, som I vänten efter.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Och I skolen åkalla mig, och gå och bedja mig, och jag skall höra eder.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 I skolen söka mig, och finna mig; ty om I mig af allt hjerta söken,
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 Så skall jag låta mig finna af eder, säger Herren; och jag skall vända edart fängelse, och församla eder utur all folk, och utaf all rum, dit jag eder utdrifvit hafver, säger Herren; och skall låta eder återkomma till detta rum igen, dädan jag eder hafver bortföra låtit.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Ty I menen, att Herren hafver uppväckt eder Propheter i Babel.
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 Ty detta säger Herren om Konungen, som på Davids stol sitter, och om allt folket, som i denna stadenom bor, nämliga om edra bröder, som med eder uti fängelset icke utdragne äro;
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Ja, så säger Herren Zebaoth: Si, jag skall sända ibland dem svärd, hunger och pestilentie, och skall så ställa mig med dem, lika som med de onda fikon, de man vämjar vid att äta;
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 Och skall förfölja dem med svärd, hunger och pestilentie, och skall icke låta dem blifva, uti något rike på jordene, så att de skola varda till bannor, till under, till hån och spott, ibland all folk, dit jag dem utdrifvandes varder;
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 Derföre, att de icke hafva hört min ord, säger Herren, de jag städse med mina tjenare Propheterna till eder sändt hafver; men I villen intet höra, säger Herren.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 Men I alle, som fångne bortförde ären, de jag hafver ifrå Jerusalem till Babel draga låtit, hörer Herrans ord.
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Detta säger Herren Zebaoth, Israels Gud, emot Achab, Kolaja son, och emot Zedekia, Maaseja son, hvilke eder lögn spå i mitt Namn: Si, jag skall gifva dem uti NebucadNezars händer, Konungens i Babel; han skall låta slå dem för edor ögon;
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 Så att man skall göra bannor af dem ibland alla fångar af Juda, som i Babel äro, och säga: Herren göre dig lika som Zedekia och Achab, hvilka Konungen af Babel på eld steka lät;
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 Derföre att de bedrefvo en galenskap i Israel, och bedrefvo hor med annars mans hustrur, och predikade lögn i mitt Namn, det jag dem intet befallt hade. Detta vet jag, och betygar det, säger Herren.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 Och emot Semaja af Nehelam skall du säga:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 Detta säger Herren Zebaoth, Israels Gud; derföre, att du under ditt namn hafver bref sändt till allt folket, som i Jerusalem är, och till Presten Zephanja, Maaseja son, och till alla Presterna, och sagt:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 Herren hafver satt dig till en Prest uti Prestens Jehojada stad, att I skolen tillsiare vara uti Herrans hus öfver alla ursinniga och spåmän, att du skall sätta dem i fångahus och i stock;
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 Och nu, hvi straffar du då icke Jeremia af Anathoth, den eder propheterar?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 Derföre, att han till oss i Babel sändt hafver, och låtit säga: Det skall ännu länge vara; bygger hus, der I uti bon, och planterer trägårdar, att I äten der frukt af.
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Och Zephanja Presten hade läsit det samma brefvet, och låtit Jeremia Propheten höra det.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Derföre skedde Herrans ord till Jeremia, och sade:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 Sänd bort till alla fångarna, och låt säga dem: Detta säger Herren emot Semaja af Nehelam: Derföre, att Semaja propheterar eder, och jag hafver dock intet sändt honom, och hafver gjort, att I förlåten eder uppå lögn;
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 Derföre säger Herren alltså: Si, jag skall hemsöka Semaja af Nehelam, samt med hans säd, så att ingen af hans skall blifva ibland detta folket, och skall icke se det goda, som jag desso mino folke göra vill, säger Herren; ty han hafver med sitt tal afvändt dem ifrå Herranom.
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremia 29 >