< Jesaja 62 >

1 För Zions skull vill jag icke tiga, och för Jerusalems skull vill jag icke hållat inne; tilldess dess rättfärdighet uppgår såsom ett sken, och dess salighet brinner såsom ett bloss;
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 Att Hedningarna måga se dina rättfärdighet, och alle Konungar dina härlighet, och du skall med ett nytt namn nämnd varda, hvilket Herrans mun nämna skall.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 Och du skall vara en skön krona uti Herrans hand; och en Konungslig hatt uti dins Guds hand.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 Man skall icke mer kalla dig den öfvergifna, ej heller ditt land ett öde; utan du skall kallas: Min lust i henne, och ditt land: Det hafver en Herra; ty Herren hafver lust till dig, och ditt land hafver en Herra.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 Ty såsom en ung man hafver ena jungfru kär, så skola din barn hafva dig kär; och såsom en brudgumme gläder sig öfver brudena, så skall ock din Gud fröjda sig öfver dig.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 O Jerusalem! jag vill beställa väktare uppå dina murar, de som icke tiga skola hvarken dag eller natt: och de som på Herran tänka skola, på det att när eder intet tyst vara skall;
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 Och I icke skolen tiga om honom, tilldess Jerusalem varder beredt, och satt till ett lof uppå jordene.
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 Herren hafver svorit vid sina högra, hand, och vid sins magts arm: Jag vill icke mer gifva dina säd dinom fiendom till att äta, ej heller din must, der du uppå arbetat hafver, de främmande dricka låta;
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 Utan de som insamla det, de skola ock ätat, och lofva Herran; och de som införat, skola dricka det uti mins helgedoms gårdar.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Går, går genom porten; bereder folkena väg; görer väg, görer väg; rödjer bort stenarna, reser ett baner upp emot folken.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 Si, Herren låter höra sig allt intill verldenes ända: Säger dottrene Zion: Si, din salighet kommer; si, hans arbete och hans verk skall icke vara utan frukt.
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 Man skall kalla dem det heliga folket, Herrans förlossade; och dig skall man kalla den besökta, och icke öfvergifna staden.
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.

< Jesaja 62 >