< Jesaja 49 >

1 Hörer mig, I öar, och I folk, som fjerran ären, gifver akt häruppå: Herren hafver kallat mig af moderlifvet; han hafver tänkt uppå mitt namn, medan jag ännu i moderlifvet var;
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 Och hafver gjort min mun såsom ett skarpt svärd; han hafver öfverskylt mig med sine hands skugga; han hafver gjort mig till en blankan pil, och stungit mig uti sitt koger;
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 Och säger till mig: Du äst min tjenare, Israel, genom hvilken jag vill prisad varda.
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Men jag tänkte: Jag arbetade fåfängt, jag hafver fåfängt och onytteliga förtärt mina kraft häruppå; ändock min sak är Herrans, och mitt ämbete hörer minom Gud till.
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Och nu, säger Herren, som mig af moderlifvet till sin tjenare beredt hafver, af jag skulle omvända Jacob till honom, på det Israel icke skulle blifva borto; derföre är jag härlig för Herranom, och min Gud är min starkhet;
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 Och säger: Det är en ringa ting, att du äst min tjenare, till att upprätta Jacobs slägter, och igenföra det förskingrada i Israel; utan jag hafver ock gjort dig till Hedningarnas ljus, att du skall vara min salighet intill verldenes ända.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Så säger Herren Israels förlossare, hans Helige, till de föraktada själar, till det folk der man styggelse vid hafver, till den tjenaren som under tyranner är: Konungar skola se och uppstå, och Förstar skola tillbedja för Herrans skull, som trofast är; för den Heligas skull i Israel, den dig utkorat hafver.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Detta säger Herren: Jag hafver bönhört dig i behagelig tid, och hafver hulpit dig på salighetenes dag, och hafver bevarat dig, och satt dig till ett förbund i folkena, att du skall upprätta landet, och intaga de förderfvada arf;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 Till att säga till de fångar: Går ut; och till dem i mörkret: Kommer fram; att de skola föda sig på vägarna, och hafva deras födo på alla högar.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 De skola hvarken hungra eller törsta; dem skall ingen hette eller solen stinga; ty deras förbarmare skall föra dem, och leda dem till vattukällor.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 Jag skall göra all mina berg till vägar, och mine stigar skola trampade varda.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Si, desse skola komma fjerranefter, och si, de andre ifrån nordan, och desse ifrån hafvet, och de andre ifrån Sinims land.
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Fröjder eder, I himlar, gläd dig, du jord, lofsäger, I berg, med fröjd; ty Herren hafver hugsvalat sitt folk, och förbarmat sig öfver sina elända.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Men Zion säger: Herren hafver öfvergifvit mig, Herren hafver förgätit mig.
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Månn ock en qvinna kunna förgäta sitt barn, så att hon icke förbarmar sig öfver sins lifs son? Och om hon än förgäten, så vill jag dock icke förgäta dig.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Si, uppå händerna hafver jag upptecknat dig. Dina murar äro alltid för mig,
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Dine uppbyggare skola skynda sig; men dine nederbrytare och förstörare skola draga sig derifrå.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Lyft din ögon upp allt omkring och se: Alle desse komma församlade till dig; så sant som jag lefver, säger Herren, du skall med allo desso, såsom med en skrud, utiklädd varda, och skall dermed omsvepa dig som en brud.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Ty ditt förödda, förstörda och förderfvade land skall då varda dig allt för trångt till att bo uti, när dine förderfvare långt ifrå dig komma;
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Så att dins ofruktsamhets barn skola ännu säga för din öron: Rummet är mig för trångt; sitt åt dig, att jag må bo när dig.
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Men du skall säga i ditt hjerta: Ho hafver mig dessa födt? Jag är ofruktsam, ensam, fördrifven och utskjuten; ho hafver mig dessa uppfödt? Si, jag var ensam öfvergifven; hvar voro då desse?
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Så säger Herren Herren: Si, jag vill upplyfta min hand till Hedningarna, och uppresa mitt baner till folken, så skola de bära dina söner fram på armarna, och draga dina döttrar på axlarna.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Och Konungar skola vara dine skaffare, och deras Förstinnor dina ammor. De skola för dig nederfalla till jordena på ansigtet, och sleka dina fötters stoft. Då skall du förnimma, att jag är Herren, på hvilkom ingen till skam varder, som hoppas uppå mig.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Kan man ock taga enom kämpa hans rof bort, eller kan man lösgöra ens rättfärdigs fångar?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Ty så säger Herren: Nu skola de fångar kämpanom borttagne varda, och dess starkas rof löst varda, och jag skall träta med dina trätare, och hjelpa dina barn.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 Och jag skall spisa dina plågare med deras eget kött, och de skola druckne varda af sitt eget blod, såsom af sött vin; och allt kött skall förnimma, att jag är Herren din Frälsare, och din förlossare, den mägtige i Jacob.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”

< Jesaja 49 >