< 1 Mosebok 46 >
1 Israel for dit med allt det honom tillhörde. Och då han kom till BerSaba, offrade han ett offer sins faders Isaacs Gudi.
Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
2 Och Gud sade till honom om nattena i ene syn: Jacob, Jacob. Han sade: Här är jag.
Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
3 Och han sade: Jag är Gud, dins faders Gud, frukta dig icke att fara in i Egypten; förty, der vill jag göra dig till ett mägtigt folk.
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
4 Jag vill fara dit med dig, och vill åter föra dig derut. Och Joseph skall lägga sina hand uppå din ögon.
Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
5 Då for Jacob ifrå BerSaba. Och Israels barn förde Jacob sin fader, med sin barn och hustrur, på vagnomen, som Pharao hade sändt till att föra dem med.
Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
6 Och togo sin boskap och håfvor, som de förvärfvat hade i Canaans lande, och kommo så in uti Egypten, Jacob och all hans säd med honom:
Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
7 Hans barn och hans barnabarn med honom, hans döttrar, och hans barns döttrar, och all hans säd.
Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
8 Desse äro Israels barns namn, de som kommo i Egypten: Jacob och hans söner. Jacobs förstfödde son Ruben.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
9 Rubens barn: Hanoch, Pallu, Hezron och Charmi.
’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
10 Simeons barn: Jemuel, Jamin, Ohad, Jachin, Zohar, och Saul den Cananeiske qvinnones son.
’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
11 Levi barn: Gerson, Kehat och Merari.
’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
12 Juda barn: Er, Onan, Sela, Perez och Serah. Men Er och Onan dödde i Canaans lande. Men Perez barn: Hezron och Hamul.
’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
13 Isaschars barn: Thola, Phuva, Job och Simron.
’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
14 Sebulons barn: Sered, Elon och Jahleel.
’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
15 Desse äro barnen af Lea, som hon födde Jacob i Mesopotamien, med sine dotter Dina: De göra tillhopa alle, med söner och döttrar, tre och tretio själar.
Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
16 Gads barn: Ziphion, Haggi, Suni, Ezbon, Eri, Arodi och Areli.
’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
17 Assers barn: Jimna, Jisua, Jisui, Brya; och Serah, deras syster. Men Bryas barn: Heber och Malchiel.
’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
18 Desse äro Silpas barn, som Laban gaf Lea sine dotter, och födde Jacob dessa sexton själar.
Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
19 Rachels Jacobs hustrus barn: Joseph och BenJamin.
’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
20 Och Joseph vordo födde i Egypten, Manasse och Ephraim, som honom födde Asnath Potiphera dotter Prestens i On.
A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
21 BenJamins barn: Bela, Becher, Asbel, Gera, Naaman, Ehi, Ros, Muppim, Huppim och Ard.
’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
22 Desse äro barnen af Rachel, som Jacob födde äro; alle tillhopa fjorton själar.
Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
Yaron Dan shi ne, Hushim.
24 Naphthali barn: Jahzeel, Guni, Jezer och Sillem.
’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
25 Desse äro Bilhas barn, som Laban hade gifvit sine dotter Rachel, och födde Jacob dessa sju själar.
Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
26 Alla själar som kommo med Jacob in i Egypten, som utgångne voro af hans länd, undantagande hans barnahustrur, äro alle tillsamman sex och sextio själar.
Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
27 Och Josephs barn, som honom vordo födde i Egypten, voro två själar: Så att alla Jacobs hus själar, som kommo in i Egypten, voro sjutio.
In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
28 Och han sände Juda för sig till Joseph, att han skulle visa honom vägen till Gosen; och de kommo in i landet Gosen.
To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
29 Då spände Joseph före sin vagn, och for ut emot Israel sin fader till Gosen. Och då han fick se honom, föll han om hans hals, och gret svårliga på hans hals.
sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
30 Då sade Israel till Joseph: Nu vill jag gerna dö, efter det jag hafver sett ditt ansigte, att du ännu lefver.
Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
31 Joseph sade till sina bröder och sin faders hus: Jag vill fara upp, och undervisa der Pharao, och säga till honom: Mine broder och mins faders hus är kommit till mig utaf Canaans land;
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
32 Och äro herdar, ty det är sådana folk, som med boskap umgå plägar; deras får och fä, och allt det de hafva, hafva de fört med sig.
Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
33 Då nu Pharao varder eder kallandes, och säger: Hvad är edar handel?
Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
34 Så skolen I säga: Dine tjenare äro folk, som med boskap umgå ifrå vår barndom allt härtill, både vi och våre fäder, på det I må få bo i det landet Gosen; förty alle herdar äro såsom en styggelse för de Egyptier.
Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”