< 1 Mosebok 39 >
1 Joseph vardt förd neder i Egypten: Och Potiphar, en Egyptisk man, Pharaos hofmästare, köpte honom af de Ismaeliter, som honom hade fört der ned.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 Och Herren var med Joseph, så att han vardt en lyckosam man: Och var i sins herras dens Egyptiens huse.
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 Och hans herre såg, att Herren var med honom; ty allt det han gjorde, lät Herren gå lyckosamlig till med honom:
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 Så att han fann nåd för sinom herra, och vardt hans tjenare: Han satte honom öfver sitt hus, och allt det han hade lät han under hans händer.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 Och ifrå den tiden, då han hade satt honom öfver sitt hus och alla sina ägodelar, välsignade Herren den Egyptiens hus för Josephs skull: Och var alltsammans Herrans välsignelse i allo de han hade, hemma och på markene.
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 Derföre lät han det allt under Josephs händer, hvad han hade; och hade intet deraf, utan allena brödet, som han åt. Och Joseph var dägelig och fager under ansigtet.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 Och det begaf sig, då detta var skedt, att hans herras hustru kastade sin ögon på Joseph, och sade: Ligg när mig.
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 Men han vägrade det henne, och sade till henne: Si, min herre vet icke hvad i hans huse är, och allt det han hafver, hafver han gifvit under mina händer.
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 Och hafver intet så godt i sino huse, det han i mitt våld icke gifvit hafver, utan dig, ty du äst hans hustru. Hvi skulle jag nu så mycket ondt göra, och synda emot Gud?
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 Men hon hade dageliga sådana ord till Joseph; men han lydde henne intet, att han skulle ligga när henne, eller vara något om henne.
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 Det begaf sig en dag, att Joseph gick in i huset till att göra sina sysslo; och ingen af husfolket var der när.
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 Och hon fick honom i hans mantel, och sade: Ligg när mig. Men han lät blifva mantelen i hennes hand, och rymde ut af huset.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 Då hon nu såg, att han lät blifva mantelen i hennes hand, och rymde ut,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 Kallade hon husfolket, och sade till dem: Si, han hafver fört oss här in en Ebreisk man, att han skulle komma oss på skam. Han kom här in till mig, på det han skulle ligga när mig; men jag ropade med höga röst.
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 Och då han hörde, att jag skriade och ropade, då lefde han sin mantel när mig, och flydde, och lopp ut.
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 Och hon lade hans mantel när sig, så länge hennes herre kom hem.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 Och talade till honom samma orden, och sade: Den Ebreiske tjenaren, som du hafver haft här in, kom här in till mig, att han skulle komma mig på skam.
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 Men då jag skriade och ropade, lefde han sin mantel när mig, och flydde ut.
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 Då hans herre hörde sådana sine hustrus ord, som hon till honom talade, och sade: Så hafver mig din Ebreiske tjenare gjort; vardt han ganska vred.
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 Då tog hans herre honom, och lade honom i fängelse, der Konungens fångar inne lågo: Och der låg han då i fängelset.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 Men Herren var med honom, och var honom gunstig, och lät honom finna nåd för befallningsmannen öfver fångahuset.
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 Så att han befallte alla fångarna i fängelsena under hans hand, att allt det der skedde, måste ske genom honom.
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 Förty befallningsmannen öfver fängelset såg, att Herren var med honom i allt det som under hans händer var, och att Herren lät, det han gjorde, lyckosammeliga tillgå.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.