< 1 Mosebok 36 >

1 Detta är Esaus slägte, som kallas Edom.
Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
2 Esau tog hustrur af Canaans döttrar: Ada Elons Hetheens dotter, och Aholibama Anas dotter, Zibeons Heveens dotters.
Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
3 Och Basmath Ismaels dotter, Nebajoths syster.
ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
4 Och Ada födde Esau Eliphas. Men Basmath födde Reguel.
Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
5 Aholibama födde Jeus, Jaelam och Korah. Desse äro Esaus barn, som honom födde voro i Canaans lande.
Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
6 Och Esau tog sina hustrur, söner och döttrar, och alla sins huses själar; sina håfvor, och allan boskapen med alla ägodelar, som han förvärfvat hade i Canaans lande: Och for uti ett land, ifrå sin broder Jacob.
Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
7 Förty deras ägodelar voro så stora, att de kunde icke bo med hvarannan: Och landet, der de uti främlingar voro, kunde icke fördraga dem, för deras stora ägodelars skull.
Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
8 Så bodde då Esau på Seirs berg: Och denne Esau är Edom.
Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
9 Detta är Esaus slägte, af hvilkom de Edomeer komne äro på Seirs berg.
Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
10 Och så heta Esaus barn: Eliphas Ada son, Esaus hustrus; Reguel Basmaths son, Esaus hustrus.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
11 Men Eliphas söner voro desse: Theman, Omar, Zepho, Gatham och Kenas.
’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
12 Och Thimna var Eliphas Esau sons frilla; hon födde Amalek. Desse äro de barn af Ada, Esaus hustru.
Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
13 Men Reguels barn äro desse: Nahath, Serah, Samma, Missa. Desse äro de barn af Basmath, Esaus hustru.
’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
14 Men de barn af Aholibama, Esaus hustru, Anas dotter, Zibeons dotters, äro desse, dem hon födde Esau: Jeus, Jaelam och Korah.
’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
15 Desse äro de Förstar ibland Esaus barn: Eliphas barn, den första Esaus sons, voro desse: den Försten Theman, den Försten Omar, den Försten Zepho, den Försten Kenas,
Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
16 Den Försten Korah, den Försten Gatham, den Försten Amalek. Desse äro de Förstar af Eliphas i Edoms lande; och äro barn af Ada.
Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
17 Och desse äro Reguels barn, Esau sons: Den Försten Nahath, den Försten Serah, den Försten Samma, den Försten Missa. Desse äro de Förstar af Reguel uti de Edomeers lande; och äro barn af Basmath, Esaus hustru.
’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
18 Desse äro barn af Aholibama, Esaus hustru: Den Försten Jeus, den Försten Jaelam, den Försten Korah. Desse äro de Förstar af Aholibama Anas dotter, Esaus hustru.
’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
19 Desse äro Esaus barn, och deras Förstar; han är Edom.
Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
20 Men de barn af Seir den Horeen, som i landena bodde, äro desse: Lotan, Sobal, Zibeon, Ana,
Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
21 Dison, Ezer och Disan. Desse äro de Förstar ibland de Horeer, alle Seirs barn i Edoms lande.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
22 Men Lotans barn voro desse: Hori och Hemam; och Lotans syster het Thimna.
’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
23 Sobals barn voro desse: Alvan, Manahat, Ebal, Sepho och Onam.
’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
24 Zibeons barn voro: Aja och Ana: Denne är den Ana, som i öknene påfann mular, då han vaktade sins faders Zibeons åsnar.
’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
25 Men Anas barn voro: Dison och Aholibama, det är Anas dotter.
’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
26 Disons barn voro: Hemdan, Esban, Jithran och Cheran.
’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
27 Ezers barn voro: Bilhan, Saavan och Akan.
’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
28 Disans barn voro: Uz och Aran.
’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
29 Desse äro de Förstar ibland de Horeer: Den Försten Lotan, den Försten Sobal, den Försten Zibeon, den Försten Ana.
Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
30 Den Försten Dison, den Försten Ezer, den Försten Disan. Desse äro de Förstar ibland de Horeer, de som regerade i Seirs lande.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
31 Men de Konungar, som i Edoms lande regerade, förra än Israels barn Konungar hade, äro desse:
Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
32 Bela var Konung i Edom, Beors son; och hans stad het Dinhaba.
Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
33 Och då Bela blef död, vardt Jobab Konung i hans stad, Seras son af Bozra.
Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
34 Då Jobab blef död, vardt Husam utaf de Themaneers lande Konung i hans stad.
Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
35 Då Husam blef död, vardt Konung i hans stad Hadad Bedads son, den som slog de Midianiter på de Moabiters mark; och hans stad het Avith.
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
36 Då Hadad blef död, vardt Samla af Masreka Konung i hans stad.
Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
37 Då Samla blef död, vardt Konung i hans stad Saul af Rehoboth vid älfvena.
Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
38 Då Saul blef död, vardt Baalhanan Achbors son Konung i hans stad.
Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
39 Då Baalhanan Achbors son blef död, vardt Hadar Konung i hans stad: Och hans stad het Pagu; och hans hustru het Mehetabeel, Matreds dotter, och Mesahabs dotter.
Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
40 Alltså heta de Förstar af Esau i deras slägter, rummom och namnom: Den Försten Thimna, den Försten Alva, den Försten Jetheth,
Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
41 Den Försten Aholibama, den Försten Ela, den Försten Pinon,
Oholibama, Ela, Finon.
42 Den Försten Kenas, den Försten Theman, den Försten Mibzar,
Kenaz, Teman, Mibzar.
43 Den Försten Magdiel, den Försten Iram. Desse äro de Förstar i Edom, såsom de bott hafva uti deras arfvelande. Och Esau är fadren till de Edomeer.
Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.

< 1 Mosebok 36 >