< 1 Mosebok 22 >

1 Sedan det skedt var, försökte Gud Abraham, och sade till honom: Abraham. Och han svarade: Här är jag.
Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
2 Och han sade: Tag Isaac din enda son, den du kär hafver, och gack bort uti Moria land, och offra honom der till ett bränneoffer på ett berg, det jag dig sägandes varder.
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
3 Då stod Abraham bittida upp om morgonen, och sadlade sin åsna, och tog med sig två drängar, och sin son Isaac, och högg sönder ved till bränneoffer, stod upp och gick bort till det rum, som Gud honom sagt hade.
Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
4 På tredje dagen hof Abraham sin ögon upp, och såg rummet långt ifrå.
A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
5 Och sade till sina drängar: Blifver I här med åsnanom, jag och pilten viljom gå dit bort, och när vi tillbedit hafvom, vilje vi komma igen till eder.
Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
6 Och Abraham tog veden till bränneoffret, och lade den på sin son Isaac: Men han tog elden och knifven i sina hand, och gingo så både tillsamman.
Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
7 Då sade Isaac till sin fader Abraham: Min fader. Abraham svarade: Här är jag, min son. Och han sade: Si, här är elden och veden, hvar är nu fåret till bränneoffret?
sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
8 Abraham svarade: Gud förser väl fåret, min son, till bränneoffret: Och de gingo både tillsamman.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
9 Och som de kommo till rummet, der Gud honom af sagt hade, byggde Abraham der ett altare, och lade veden deruppå; bandt sin son Isaac, och lade honom på altaret, ofvan på veden.
Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
10 Och uträckte sina hand, och tog till knifven, att han skulle slagta sin son.
Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
11 Då ropade honom Herrans Ängel af himmelen och sade: Abraham, Abraham. Han svarade: Här är jag.
Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
12 Han sade: Kom intet dina hand vid pilten, och gör honom intet; ty nu vet jag att du fruktar Gud, och hafver icke skonat din enda son för mina skull.
Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
13 Då hof Abraham sin ögon upp, och såg en vädur bak sig, bekajad med hornen uti en törnebuska: Och gick dit, och tog den väduren, och offrade honom till ett bränneoffer i sins sons stad.
Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
14 Och Abraham kallade det rummet, Herren ser; af hvilko man ännu i dag säger: På berget, der Herren sedd varder.
Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
15 Och Herrans Ängel ropade åter till Abraham af himmelen,
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16 Och sade: Jag hafver svorit vid mig sjelf, säger Herren, efter du detta gjorde, och icke skonade din enda son,
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17 Att jag skall välsigna, och föröka dina säd såsom stjernorna på himmelen, och såsom sanden på hafsens strand: Och dina säd skall besitta sina fiendars portar.
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18 Och i dine säd skall allt folk på jordene välsignadt varda; derföre, att du mine röst lydt hafver.
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19 Sedan gick Abraham till drängarna igen, och gjorde sig redo, och drogo tillsammans till BerSaba, och bodde der.
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
20 Då detta så skedt var, begaf sig, att Abraham vardt sagdt: Si, Milca hafver ock födt barn dinom broder Nahor;
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
21 Nemliga Uz den förstfödda, och Bus hans broder, och Kemuel, af hvilkom de Syrier komne äro:
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22 Och Kesed, och Haso, och Pildas, och Jidlaph, och Bethuel.
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23 Men Bethuel födde Rebecka. Dessa åtta födde Milca Nahor, Abrahams broder.
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
24 Och hans frilla benämnd Rehuma födde ock, nemliga Tebah, Gaham, Thahas och Maacha.
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.

< 1 Mosebok 22 >