< 1 Mosebok 18 >
1 Och Herren syntes honom i dem lundenom Mamre, der han satt vid sins tjälls dörr, då hetast var på dagenom.
Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
2 Och som han upplyfte sin ögon och såg, då stodo tre män för honom. Och då han såg dem, lopp han emot dem ifrå sins tjälls dörr, och bugade sig ned på jordene.
Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
3 Och sade: Herre, hafver jag funnit nåd för din ögon, så gack icke fram om din tjenare.
Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
4 Man vill hemta eder litet af vatten och två edra fötter, och hviler eder under trät.
Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
5 Och jag vill lägga för eder ett stycke bröd, att I vederqvecken edor hjerta; sedan gån I då fram bätter, förty derföre ären I komne till edar tjenare. De sade: Gör som du hafver sagt.
Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
6 Abraham skyndade sig in i tjället till Sara, och sade henne: Skynda dig, och blanda tre mått semlomjöl, och baka kakor.
Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
7 Men han lopp bort till boskapen, och tog en god späd kalf, och fick drängenom; han skyndade sig, och tillredde det.
Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
8 Och han tog fram smör och mjölk, och af kalfvenom, som han tillredt hade, och satte för dem; och gick fram för dem under trät, och de åto.
Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
9 Då sade de till honom: Hvar är din hustru Sara? Han svarade: Derinne i tjället.
Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
10 Han sade: När jag igenkommer till dig, om man lefver, si, så skall Sara din hustru hafva en son. Detta hörde Sara, der hon stod bak tjälldörrena.
Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
11 Och de voro, både Abraham och Sara, gamle och väl till ålders komne, så att Sara nu icke mer hade som qvinnor pläga hafva.
Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
12 Derföre log hon vid sig sjelf, och sade: Nu jag gammal är, och min herre desslikes ålderstigen, skall jag ännu gifva mig till lusta?
Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
13 Då sade Herren till Abraham: Hvi log Sara, sägandes: Menar du, att det kan vara, att jag ännu föda skall, så gammal som jag är?
Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
14 Mån Herranom något vara omöjeligit? I sinom tid vill jag komma till dig igen, om man lefver, och då skall Sara hafva en son.
Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
15 Då nekade Sara, och sade: Jag log intet, och vardt förfärad. Men han sade: Det är icke så, du logst.
Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
16 Då stodo männerne upp dädan, och vände sig åt Sodom, och Abraham följde dem och ledsagade dem.
Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
17 Och Herren sade: Huru kan jag dölja för Abraham det jag gör?
Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
18 Efter han skall varda till ett stort och mägtigt folk, och all folk på jordene skola varda välsignade i honom.
Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
19 Ty jag vet, att han befaller sinom barnom, och sino huse efter sig, att de skola hålla Herrans vägar, och göra hvad rätt och godt är, på det att Herren skall låta komma öfver Abraham allt det han honom lofvat hafver.
Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
20 Och Herren sade: I Sodom och Gomorra är ett rop, det är stort, och deras synder äro ganska svåra.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
21 Derföre skall jag fara ned och se till, om de allt gjort hafva efter ropet, som för mig kommet är; eller om det icke så är, att jag må vetat.
zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
22 Och männerne vände sitt ansigte, och gingo åt Sodom. Men Abraham vardt ståndandes för Herranom.
Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
23 Och trädde fram till honom, och sade: Vill du då förgöra den rättfärdiga med den ogudaktiga?
Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
24 Kunde hända, att i stadenom voro femtio rättfärdige, ville du dem förgöra, och icke skona de rummena för femtio rättfärdigas skull, som derinne voro?
Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
25 Bort det ifrå dig, att du det göra skulle, och döda den rättfärdiga med den ogudaktiga, och att dem rättfärdiga skulle gå lika som de ogudaktiga; bort det ifrå dig, som alla verldenes domare äst, sådana straff låter du icke gå.
Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
26 Herren sade: Finner jag femtio rättfärdiga i Sodoms stad, så vill jag skona allestäds i all rum för deras skull.
Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
27 Abraham svarade och sade: Ack si, jag hafver tagit mig före att tala med Herranom, ändock jag är stoft och aska.
Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
28 Om der voro fem mindre än femtio rättfärdige inne, ville du då förgöra hela staden för de fems skull? Han sade: Finner jag derinne fem och fyratio, så vill jag icke förgöra dem.
in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
29 Och han talade ändå ytterligare till honom, och sade: Måtte hända, att man finner der fyratio inne. Och han sade: Jag vill intet göra dem för de fyratio skull.
Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
30 Och Abraham sade: Herre, tag icke till misstycke, om jag ännu talar något: Måtte hända, att man finner der tretio inne. Han svarade: Finner jag der tretio inne, så vill jag intet göra dem.
Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
31 Och han sade: Ack si, jag hafver tagit mig före att tala med min Herra: Måtte hända, att man finner tjugu derinne. Han svarade: Jag vill icke förgöra dem för de tjugu skull.
Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
32 Och han sade: Tag icke till misstycke, Herre, om jag talar än en tid: Måtte hända, att man finner tio derinne. Han sade: Jag vill icke förgöra dem för de tio skull.
Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
33 Och Herren gick bort, sedan han hade uttalat med Abraham; och Abraham vände om och gick hem till sitt igen.
Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.