< Galaterbrevet 2 >

1 Sedan, efter fjorton år, for jag åter upp till Jerusalem med Barnaba, och tog Titum ock med mig.
Bayan shekara goma sha huɗu sai na sāke haurawa zuwa Urushalima, a wannan lokaci na tafi tare da Barnabas. Na kuma ɗauki Titus muka tafi tare.
2 Och for jag dit upp efter en uppenbarelse, och befrågade mig med dem om Evangelium, som jag förkunnar ibland Hedningarna; besynnerliga med dem, som för något voro räknade; på det jag icke skulle löpa fåfängt, eller redo lupit hafva.
Na tafi ne bisa ga wani wahayi. Da na kai can, sai na bayyana musu bisharar da nake wa’azi a cikin Al’ummai. Na yi haka a keɓance a gaban waɗanda suke shugabanni, don tsoro kada gudun da nake yi, ko kuwa na riga na yi, yă zama a banza.
3 Men icke vardt heller Titus, som med mig var, nödgad till att låta omskära sig, ändock han var en Grek.
Amma ko Titus ma da yake tare da ni, ba a ce dole sai ya yi kaciya ba, ko da yake shi mutumin Al’ummai ne.
4 Ty då någre falske bröder sig med inträngde, och med inkomne voro, till att bespeja vår frihet, som vi hafve i Christo Jesu, på det de skulle komma oss i träldom;
Wannan zancen kaciya ya taso domin waɗansu’yan’uwan ƙarya sun shiga cikinmu domin su yi leƙe a kan’yancin da muke da shi a cikin Kiristi Yesu, su kuma mai da mu bayi.
5 Vekom vi för dem icke en stund till underdånighet; på det Evangelii sanning skulle blifva beståndandes när eder.
Ba mu kuwa ba su zarafi ba ko kaɗan, don gaskiyar bishara ta ci gaba da kasance tare da ku.
6 Men af dem som något räknade voro, hurudane de fordom varit hade, det kommer mig intet vid; Gud aktar icke menniskones anseende; men de som något voro räknade, lärde mig intet;
Game da waɗanda aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne, ko wane ne su, duk ɗaya ne a wurina; gama Allah ba ya nuna bambanci, ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙara mini kome ba.
7 Utan heldre tvärtemot; då de sågo, att mig betrodt var Evangelium till förhuden, lika som Petro till omskärelsen;
A maimakon haka, sun ga cewa an danƙa mini hakkin wa’azin bishara ga Al’ummai, kamar yadda aka danƙa wa Bitrus ga Yahudawa.
8 (Ty den som med Petro var kraftig till Apostla-ämbetet ibland omskärelsen, den hafver ock med mig kraftig varit ibland Hedningarna; )
Gama Allah wanda ya yi aiki a cikin hidimar Bitrus a matsayin manzo ga Yahudawa, haka ma ya yi aiki a cikin hidimata a matsayin manzo ga Al’ummai.
9 Och förnummo den nåd, som mig gifven var, räckte Jacobus och Cephas, och Johannes, hvilke såsom pelare räknade voro, mig och Barnabe handena, och förenade sig med oss, så att vi skulle predika ibland Hedningarna, och de ibland omskärelsen;
Yaƙub, Bitrus da Yohanna waɗanda suke fitattun ginshiƙai, sun karɓe ni da Barnabas da hannu biyu biyu sa’ad da suka gane alherin da aka ba ni. Suka kuma yarda cewa ya kamata mu tafi wajen Al’ummai, su kuwa su tafi wajen Yahudawa.
10 Allenast, att vi skulle tänka på de fattiga; hvilket jag också hafver vinnlagt mig att göra.
Abin da dai suka roƙa shi ne ya kamata mu riƙa tuna da matalauta, abin nan da nake marmarin yi.
11 Men då Petrus kom till Antiochien, stod jag honom uppenbarliga emot; ty klagomål var kommen öfver honom.
Sa’ad da Bitrus ya zo Antiyok, na tsawata masa ido da ido don laifinsa a fili yake.
12 Ty förr än någre voro komne ifrå Jacobo, åt han med Hedningarna; men då de kommo, unddrog han sig, och skiljde sig ifrå dem; ty han fruktade dem som voro af omskärelsen.
Kafin waɗansu mutane su zo daga wurin Yaƙub, yakan ci abinci tare da Al’ummai. Amma da suka iso, sai ya fara janyewa, ya kuma ware kansa daga wajen Al’ummai domin yana tsoron waɗanda suke ƙungiyar masu kaciya.
13 Och de andre Judar skrymtade ock med honom, så att Barnabas vardt ock bedragen till att skrymta med dem.
Sauran Yahudawa suka haɗa kai da shi a munafuncinsa har Barnabas ma ya bauɗe.
14 Men då jag såg, att de icke rätteliga vandrade efter Evangelii sanning, sade jag till Petrum uppenbarliga för allom: Medan du, som äst en Jude, lefver som en Hedning, och icke som en Jude, hvarföre tvingar du då Hedningarna till att lefva efter Judasättet?
Da na ga cewa ba sa yin daidai da gaskiyar bishara, sai na ce wa Bitrus a gabansu duka, “Kai mutumin Yahuda ne, duk da haka kana rayuwa kamar Ba’al’umme ba kamar mutumin Yahuda ba. To, yaya aka yi, kana tilasta Al’ummai su bi al’adun Yahudawa?
15 Ändock vi af naturen äre Judar, och icke syndare af Hedningomen;
“Mu da muke Yahudawa ta wurin haihuwa ba Al’ummai masu zunubi ba,
16 Likväl, efter vi vete, att menniskan icke varder rättfärdig genom lagsens gerningar, utan genom trona på Jesum Christum, så tro vi ock på Christum Jesum, att vi skole rättfärdige varda genom trona på Christum, och icke af lagsens gerningar; derföre att intet kött varder rättfärdigadt genom lagsens gerningar.
mun san cewa mutum ba ya samun kuɓuta ta wurin kiyaye Doka, sai dai ta wurin bangaskiya cikin Kiristi Yesu. Saboda haka, mu ma, muka sa bangaskiyarmu cikin Kiristi Yesu don mu sami kuɓuta ta wurin bangaskiya cikin Kiristi ba ta wurin kiyaye Doka ba, domin ba wanda zai kuɓuta ta wurin bin Doka.
17 Men skulle vi, som söke varda rättfärdige genom Christum, ock ännu sjelfve finnas vara syndare, så vore Christus en syndatjenare. Bort det.
“In kuwa ya zama muna so mu sami zaman marasa laifi a gaban Allah ta wurin dogara ga Kiristi, sa’an nan an same mu mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, ko wannan zai nuna Kiristi yana ƙarfafa zunubi ke nan? A’a, ko kusa!
18 Ty om jag bygger det samma upp igen, som jag nederslagit hade, så gör jag mig sjelf till en öfverträdare.
In na sāke gina abin da na rushe, na zama mai karyar Doka ke nan.
19 Men jag är genom lag död ifrå lagen, på det jag skall lefva Gudi; jag är korsfäst med Christo;
“Gama ta wurin Doka na mutu ga Doka saboda in rayu ga Allah.
20 Men jag lefver, dock icke nu jag, utan Christus lefver i mig; ty det jag nu lefver i köttet, det lefver jag i Guds Sons tro, den mig älskat hafver, och gifvit sig sjelf ut för mig.
An gicciye ni tare da Kiristi. Yanzu ba ni ne nake raye ba, Kiristi ne yake raye a cikina. Rayuwar da nake yi a jiki, ina rayuwa ce ta wurin bangaskiya cikin Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni ya kuma ba da kansa domina.
21 Jag bortkastar icke Guds nåd; ty om rättfärdigheten kommer af lagen, så är Christus fåfängt död.
Ba na ajiyar alherin Allah a gefe, gama da a ce ana samun adalci ta wurin Doka, ai, da Kiristi ya mutu a banza ke nan!”

< Galaterbrevet 2 >