< Hesekiel 31 >

1 Och det begaf sig i ellofte årena, på första dagen i tredje månadenom, skedde Herrans ord till mig, och sade:
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Du menniskobarn, säg till Pharao, Konungen i Egypten, och till allt hans folk: Huru stor menar du då att du äst?
“Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
3 Si, Assur var lika som ett cedreträ på Libanon, med sköna grenar, och tjockt af löf, och ganska högt, så att dess skate stod högt upp ibland stora tjocka qvistar.
Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
4 Det hade vatten nog, att det högt vardt, och många källor, att det starkt vardt; dess strömmar gingo allt omkring dess rot, och dess bäcker till all trä i skogenom.
Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
5 Derföre är det högre vordet än all trä på markene, och fick många grenar och långa qvistar; ty det hade vatten nog till att utbreda sig.
Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
6 Alle himmelens foglar bodde uppå dess qvistar, och all vilddjur hade ungar under dess grenar, och under dess skugga bodde mång och stor folk.
Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
7 Det hade sköna, stora och långa grenar; ty dess rot hade mycket vatten.
Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
8 Och intet cedreträ var desso likt i Guds lustgård; furoträn voro dess grenom intet liknande, och mandelträn voro intet emot dess qvistar; ja, det var så dägeligit, att det öfvergick all trä i Guds lustgård.
Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
9 Jag hafver gjort det så skönt, att det fick så många qvistar, att all lustig trä i Guds lustgård båro afund dervid.
Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
10 Derföre säger Herren Herren alltså: Efter han så hög vorden är, att hans skate stod ibland stora, höga, tjocka qvistar, och hans hjerta upphof sig, att han så hög var;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
11 Derföre hafver jag gifvit honom dem mägtigasta ibland Hedningarna i händer; han skall vara till verka med honom, och fördrifvan, såsom han med sitt ogudaktiga väsende förtjent hafver;
na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
12 Att främmande skola utrota honom, nämliga Hedningarnas tyranner, och förskingra honom, att hans qvistar skola ligga på all berg, och i alla dalar, och hans qvistar sönderbrutne vid alla bäcker i landena, så att all folk på jordene måste bortdraga undan hans skugga, och öfvergifva honom.
kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
13 Och alle himmelens foglar såto på hans kullfallna bål, och all vilddjur lade sig på hans afhuggna qvistar;
Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
14 På det härefter intet trä vid vatten skall förhäfva sig af sine höjd, att dess skate ibland stora, tjocka qvistar står, och att intet trä vid vatten skall förhäfva sig öfver de andra; ty de måste alle under jordena, och dödenom öfvergifne varda, lika som andra menniskor, de der uti kulona fara.
Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
15 Detta säger Herren Herren: På den tiden, då han nederfor till helvetes, då gjorde jag en klagolåt, att djupet öfvertäckte honom, och hans strömmar måste stilla stå, och de stora vattnen intet löpa kunde; och gjorde det så, att Libanon sörjde öfver honom, och all trä i markene förtorkades öfver honom. (Sheol h7585)
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol h7585)
16 Jag förskräckte Hedningarna, då de hörde honom falla, då jag nederstörte honom till helvetes, med dem som uti kulona fara; och all lustig trä under jordene unte honom det väl, de ädlesta och bästa på Libanon, och all de som vid vatten ståndit hade. (Sheol h7585)
Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol h7585)
17 Ty de måste ock med honom neder åt helvetet, till de slagna med svärd, efter de under hans arms skugga ibland Hedningarna bott hade. (Sheol h7585)
Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol h7585)
18 Huru stor menar du då att du äst, med ditt prål och härlighet, ibland de lustiga trän? Ty du måste med de lustiga trän fara neder under jordena, och ligga ibland de oomskorna, hvilke med svärd slagne äro; alltså skall det gå dig, Pharao, med allo dino folke, säger Herren Herren.
“‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Hesekiel 31 >