< 2 Mosebok 18 >

1 Och då Jethro, Presten i Midian, Mose svär, hörde allt det Gud gjort hade med Mose och hans folk Israel, att Herren hade fört Israel utur Egypten;
Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
2 Tog han Zipora, Mose hustru, den han hade tillbakasändt;
Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
3 Samt med hennes två söner; af hvilkom en het Gersom, ty han sade: Jag är vorden en utländning i främmande lande;
da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
4 Och den andre Elieser, ty han sade: Mins faders Gud hafver varit min hjelp, och hafver frälst mig ifrå Pharaos svärde.
ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
5 Då nu Jethro, Mose svär, och hans söner, och hans hustru kommo till honom i öknene in på Guds berg, der han lägret uppslagit hade;
Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
6 Lät han säga Mose: Jag Jethro, din svär, är kommen till dig; och din hustru, och både hennes söner med henne.
Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
7 Då gick Mose ut emot honom, och böjde sig för honom, och kysste honom. Och då de hade helsat hvarannan, gingo de in i tjället.
Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
8 Då förtäljde Mose sinom svär allt det Herren hade gjort Pharao och de Egyptier, för Israels skull; och all den mödo, som de på vägenom haft hade, och att Herren hade hulpit dem.
Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
9 Och Jethro fröjdade sig öfver allt det goda, som Herren hade gjort Israel; att han hade frälst dem ifrå de Egyptiers hand.
Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
10 Och Jethro sade: Lofvad vare Herren, den eder frälst hafver ifrå de Egyptiers och Pharaos hand; den der kan frälsa sitt folk ifrå Egypti hand.
“Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
11 Nu vet jag, att Herren är större än alle gudar; derföre att de högmodeliga emot dem handlat hafva.
Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
12 Och Jethro, Mose svär, tog bränneoffer, och offrade det Gudi. Då kom Aaron, och alle de äldste i Israel, till att äta bröd för Gudi med Mose svär.
Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
13 Den andra morgonen satte sig Mose till att döma folket; och folket stod omkring Mose ifrå morgonen intill aftonen.
Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
14 Då hans svär såg allt det han gjorde med folkena, sade han: Hvad är det du gör med folkena? Hvi sitter du allena, och allt folket står omkring dig ifrå morgonen allt intill aftonen?
Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
15 Mose svarade honom: Folket kommer till mig, och frågar Gud om råd;
Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
16 Ty då de hafva något att skaffa, komma de till mig, att jag skall döma emellan hvar och en och hans nästa; och visa dem Guds rätt, och hans lag.
Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
17 Hans svär sade till honom: Det är icke godt som du gör.
Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
18 Du gör ovisliga; så ock folket, som med dig är. Detta ärendet är dig för svårt, du kan icke uträtta det allena.
Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
19 Men hör mina röst; jag vill gifva dig råd, och Gud skall vara med dig. Sköt du folket inför Gud, och framsätt ärenden för Gudi;
Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
20 Och förse dem med rätt och lag, att du visar dem den väg, der de uti vandra skola, och de gerningar, som de göra skola.
Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
21 Men sök dig upp ibland allt folket redeliga män, de som frukta Gud, sannfärdiga, och de som hata girighetena; dem sätt öfver dem, somliga öfver tusende, öfver hundrade, öfver femtio, och öfver tio;
Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
22 De som alltid måga döma folket; men när någon svår sak är, att de må hafva henne inför dig, och de åtskilja alla de ringa saker; så varder det dig lättare, och de dragat med dig.
Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
23 Om du det gör, kan du bestå hvad Gud dig bjuder; och allt detta folket kan gå hem till sitt igen med frid.
In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
24 Mose hörde sins svärs röst, och gjorde allt, såsom han sade honom;
Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
25 Och utvalde redeliga män utaf hela Israel, och gjorde dem till höfdingar öfver folket; somliga öfver tusende, öfver hundrade, öfver femtio, och öfver tio;
Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
26 Att de alltid skulle döma folket; men hvad svåra saker voro, dem sköto de till Mose; och de ringa saker dömde de.
Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
27 Och så lät Mose sin svär fara hem i sitt land igen.
Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.

< 2 Mosebok 18 >