< 2 Mosebok 10 >
1 Och Herren sade till Mose: Gack in till Pharao; ty jag hafver förhärdat hans och hans tjenares hjerta, på det jag skall göra dessa min tecken ibland dem;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 Och att du skall förkunna i din barnas öron, och din barnabarnas, hvad jag bedrifvit hafver i Egypten; och huru jag hafver bevisat min tecken ibland dem, att I skolen veta, att jag är Herren.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Så gingo Mose och Aaron in till Pharao, och sade till honom: Detta säger Herren de Ebreers Gud: Huru länge vill du icke ödmjuka dig för mig, att du släpper mitt folk till att tjena mig?
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Vill du icke släppa mitt folk, si, så vill jag i morgon låta komma gräshoppor i alla dina landsändar;
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Så att de skola öfvertäcka landet, så att man icke skall se landet, och de skola uppäta hvad eder qvart blifvet och undsatt är för haglena, och skola uppäta all edor grödande trä på markene;
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Och skola uppfylla all din hus, och alla dina tjenares hus, och alla Egyptiers hus, hvilkas like dine fäder, och dina fäders fäder icke sett hafva, ifrå den tid de på jordena kommo, intill denna dag. Och han vände sig, och gick ut ifrå Pharao.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Då sade Pharaos tjenare till honom: Huru länge skole vi lida dessa plågor? Låt folket gå, att de måga tjena Herranom sinom Gud; vetst du icke ännu, att Egypten är förderfvad?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Så vordo Mose och Aaron igen kallade till Pharao, och han sade till dem: Går åstad, och tjener Herranom edrom Gud. Hvilke äro nu de som gå skola?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Mose sade: Vi vilje gå med unga och gamla, med söner och döttrar, med får och fä; ty vi hafve en Herrans högtid.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Han sade till dem: Rätt så, Herren vare med eder. Skulle jag släppa eder och edor barn dertill? Ser der, om I icke hafven något ondt för händer?
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Icke så, utan I män går åstad, och tjener Herranom; ty det samma hafven I ock begärat. Och de drefvo dem ut ifrå Pharao.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Då sade Herren till Mose: Räck ut dina hand öfver Egypti land om de gräshoppor, att de komma öfver Egypti land, och äta allan grödan upp i landena, med allt det som qvart blifvet är efter haglet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Mose räckte sin staf öfver Egypti land, och Herren dref ett östanväder i landet i den hela dagenom, och i den hela nattene. Och om morgonen förde det östanvädret gräshopporna fram.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Och de kommo öfver hela Egypti land, och gåfvo sig ned allestäds i Egypten, så ganska många, att tillförene deras like intet varit hade ej heller härefter varder.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 Förty de öfvertäckte landet, och gjorde det svart. Och de åto upp allan grödan i landena, och all frukt på trän, som qvar var blifven efter haglet, och läto intet grönt blifva qvart på trän, och uppå grödan på markene i hela Egypti lande.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Då kallade Pharao hasteliga Mose och Aaron, och sade: Jag hafver syndat emot Herran edar Gud, och emot eder.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Förlåter mig mina synder ännu i denna resone, och beder Herran edar Gud, att han dock borttager denna döden ifrå mig.
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Och han gick ut ifrå Pharao, och bad Herran.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Då vände Herren ett ganska starkt vestanväder, och upptog gräshopporna, och förde dem i röda hafvet; så att der icke blef en qvar någorstäds i hela Egypti land.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Men Herren förstockade Pharaos hjerta, att han icke släppte Israels barn.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Herren sade till Mose: Räck dina hand upp åt himmelen, att det varder så mörkt i Egypti land, att man må taga uppå det.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Och Mose räckte sina hand upp åt himmelen; då vardt ett tjockt mörker i hela Egypti lande i tre dagar;
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 Så att ingen såg den andra, ej heller uppstod af det rummet, der han var, i de tre dagar. Men när alla Israels barn var ljust, der de bodde.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Då kallade Pharao Mose, och sade: Går åstad, och tjener Herranom, allenast låter edor får och fä blifva här; låter ock edor barn gå med eder.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Mose sade: Du måste ock låta oss hafva offer och bränneoffer, det vi Herranom vårom Gud göra skolom.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 Vår boskap skall gå med oss, och icke en klöf tillbakablifva; förty af våro skole vi taga Herranom vårom Gudi till tjenst; ty vi vete icke, hvarmed vi skole tjena Herranom, tilldess vi komme dit.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Men Herren förstockade Pharaos hjerta, att han icke ville släppa dem.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Och Pharao sade till honom: Gack ifrå mig, och tag dig vara, att du icke mer kommer för min ögon; ty hvilken dag du för mina ögon kommer, skall du dö.
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Mose svarade: Såsom du sagt hafver; jag vill ej mer komma för din ögon.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”