< Ester 7 >
1 Då Konungen kom neder med Haman till måltiden, som Drottningen Esther tillredt hade,
Saboda haka sarki da Haman suka tafi cin abinci wurin sarauniya Esta.
2 Sade Konungen till Esther, på den andra dagen, då han vin druckit hade: Hvad bedes du, Drottning Esther, det man dig gifva må? Och hvad begärar du? Ja, ock halfva riket, det skall ske dig.
Yayinda suke shan ruwan inabi a rana ta biyun nan, sai sarki ya sāke tambaya, “Sarauniya Esta, me kike so? Za a ba ki. Mene ne roƙonki? Ko da rabin masarautata ne, za a ba ki.”
3 Drottningen Esther svarade, och sade: Hafver jag funnit nåd för dig, o Konung, och om Konungenom så täckes, så gif mig mitt lif för mina böns skull, och mitt folk för mitt begärs skull.
Sai Sarauniya Esta ta amsa ta ce, “In na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, in kuma mai girma ya yarda, a bar ni da raina, wannan shi ne roƙona. Ka kuma sa kada a kashe mutanena, wannan ita ce bukata.
4 Ty vi äro sålde, jag och mitt folk, till att vi skole förgöras, slås ihjäl och förläggas; Gud gifve, att vi dock hade till trälar och trälinnor sålde varit, så ville jag hafva tegat; och hade då fienden icke gjort Konungenom skada.
Gama an sayar da ni da mutanena don a hallaka, a karkashe mu, a kuma ƙi mu. Da a ce an sayar da mu kamar bayi maza da mata ne, da na yi shiru, domin wannan zai zama abin da bai taka kara ya karye ba, har da za a dami sarki a kai.”
5 Konungen Ahasveros talade, och sade till Drottningen Esther: Hvilken är den? Eller ho är den som sådant tör sätta sig i sinnet att göra?
Sarki Zerzes ya tambayi Sarauniya Esta ya ce, “Wane ne shi? Ina mutumin da ya yi ƙarfin halin yin wannan karambani?”
6 Esther sade: Den fienden och hataren är denne onde Haman. Men Haman vardt förskräckt för Konungenom och Drottningene.
Esta ta ce, “Maƙiyi da abokin gāban, shi ne wannan mugun Haman.” Sai Haman ya tsorota a gaban sarki da sarauniya.
7 Och Konungen stod upp ifrå måltidene, och ifrå vinet, i sine grymhet, och gick in uti trägården vid huset; och Haman stod upp, och bad Drottningena Esther om sitt lif; ty han såg, att honom var ondt beredt af Konungenom.
Sarki ya tashi cikin fushi, ya bar ruwan inabinsa, ya fita zuwa cikin lambun fada. Amma da Haman ya gane cewa sarki ya riga ya yanke shawara a kan ƙaddararsa, ya dakata domin yă roƙi sarauniya Esta saboda ransa.
8 Och då Konungen kom åter igen af trägårdenom vid huset, in uti salen, der man ätit hade, lutade Haman inpå bänken, der Esther på satt. Då sade Konungen: Vill han ock öfverfalla Drottningena här i husena när mig? Då det ordet gick utu Konungens mun, förskylde de Hamans ansigte.
Sarki yana dawowa daga lambun fada zuwa babban zauren liyafan ke nan, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sarki ya tā da murya da ƙarfi ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya yayinda take tare da ni a cikin gida?” Sarki bai ma rufe baki ba, sai bayin sarki suka rufe fuskar Haman.
9 Och Harbona, en af kamererarena inför Konungenom, sade: Si, uti Hamans hus står en galge femtio alnar hög, som han till Mardechai gjort hafver, hvilken för Konungenom godt talat hafver. Konungen sade: Låt hänga honom deruti.
Sai Harbona, ɗaya daga cikin bābānni masu yi wa sarki hidima ya ce, “Akwai wurin rataye mai laifi da tsayinsa ya kai ƙafa saba’in da biyar yana nan tsaye kusa da gidan Haman. Ya gyara shi ne domin a rataye Mordekai, wanda ya yi cece sarki wanda ya tone makircin masu niyya su hallaka sarki.” Sai sarki ya ce, “Ku rataye shi a kansa!”
10 Alltså hängde man Haman i galgan, som han till Mardechai gjort hade. Sedan saktade sig Konungens vrede.
Saboda haka suka rataye Haman a kan wurin rataye mai laifin da shi Haman ya shirya saboda Mordekai. Sa’an nan sarki ya huce.