< 5 Mosebok 34 >

1 Och Mose gick utaf de Moabiters mark, upp på berget Nebo, uppå klinten af berget Pisga, tvärtemot Jericho; och Herren viste honom det hela landet Gilead, allt intill Dan;
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 Och hela Naphthali, och Ephraims land, och Manasse, och hela Juda land, allt intill det yttersta hafvet;
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 Och söderut, och den breda ängden vid Jericho Palma stadsens, allt intill Zoar.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 Och Herren sade till honom: Detta är det landet, som jag Abraham, Isaac och Jacob, svorit hafver, och sagt: Jag skall gifva det dine säd. Du hafver nu sett det med din ögon; men du skall icke komma ditöfver.
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 Och så blef Mose Herrans tjenare der död i de Moabiters lande, efter Herrans ord.
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 Och han begrof honom uti dalenom uti de Moabiters lande, emot Peors hus; och ingen hafver fått veta hans graf allt intill denna dag.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 Och Mose var hundrade och tjugu år gammal, då han blef död; hans ögon voro intet mörk vorden, och hans kinder voro intet förfallna.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 Och Israels barn begreto Mose på de Moabiters mark i tretio dagar; och de gråto- och klagodagar öfver Mose vordo fullkomnade.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 Men Josua, Nuns son, vardt uppfylld med vishetsanda; ty Mose hade lagt sina händer på honom; och Israels barn lydde honom, och gjorde såsom Herren budit hade Mose.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 Och sedan stod ingen Prophete upp i Israel, såsom Mose, den Herren kände ansigte mot ansigte;
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 Till allahanda tecken och under, till hvilken Herren honom sände, att han dem göra skulle i Egypti land, på Pharao och alla hans tjenare, och på allt hans land;
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 Och till all den mägtiga hand, och stora syner, som Mose gjorde för hela Israels ögon.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.

< 5 Mosebok 34 >