< Daniel 3 >
1 Konung NebucadNezar lät göra ett gyldene beläte, sextio alnar högt, och sex alnar bredt; och lät sätta det i Babels land på en skön plan.
Sarki Nebukadnezzar ya yi gunkin zinariya, tsawonsa kamu tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tara ne, ya kafa shi a filin Dura a yankin Babilon.
2 Och Konung NebucadNezar sände efter Förstar, herrar, landshöfdingar, domare, fogdar, rådherrar, ämbetsmän, och alla väldiga i landet, att de skulle komma tillsammans, och viga det belätet, som Konungen NebucadNezar hade uppsätta låtit.
Sa’an nan ya aika a kira hakimai da wakilai da gwamnoni da mashawarta, da ma’aji, da alƙalai, da marubutan kotu, da dukan sauran ma’aikatan yankunan, suka hallara domin a rusuna wa wannan siffar da ya kafa.
3 Då kommo Förstarna, herrarna, landshöfdingarna, domarena, fogdarna, rådherrarna, ämbetsmännerna, och alle väldige i landet tillsamman, till att viga belätet som Konung NebucadNezar hade uppsätta låtit, och de måste gå fram för belätet som NebucadNezar hade uppsätta låtit.
Saboda haka sai hakimai, da wakilai da gwamnoni, mashawarta da ma’aji da alƙalai, da marubutan alƙalai, da kuma dukan ma’aikatan yankunan suka tattaru domin kaddamar da siffar da Nebukadnezzar ya kafa, suka kuma tsaya a gabansa.
4 Och härolden ropade öfverljudt: Det låter eder sagdt vara, I all folk, slägter och tungomål;
Sai mai shela ya daga murya da ƙarfi ya ce, “Wannan shi ne abin da aka umarce ku ku yi, ya ku mutane da al’umma da kowane yare.
5 Att, när I hören basuner, trummeter, harpor, gigor, psaltare, lutor och allahanda strängaspel, så skolen I nederfalla, och tillbedja det gyldene belätet, som Konung NebucadNezar hafver uppsätta låtit.
Da zarar kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya da goge da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe ku rusuna ku yi sujada ga wannan gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
6 Men den som då icke nederfaller och tillbeder, han skall på samma stund kastas uti en brinnande ugn.
Duk wanda bai rusuna ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a cikin tendarun wuta.”
7 Då de nu hörde ljudet af basuner, trummeter, gigor, psaltare och allahanda strängaspel, föllo neder all folk, slägter och tungomål, och tillbådo det gyldene belätet, som Konungen NebucadNezar hade uppsätta låtit.
Saboda haka, da zarar suka ji karar ƙaho, da sarewa, garaya da goge da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe da kowane irin kaɗe-kaɗe kowane mutum da ko wace al’umma da kowane irin yare suka sunkuya suka yi sujada ga wannan siffa ta zinariya da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
8 Straxt på samma stund gingo någre Chaldeiske män fram, och anklagade Judarna;
A wannan lokaci sai waɗansu masanan taurari suka zo gaba suka yi karar Yahudawa.
9 Begynte, och sade till Konungen NebucadNezar: Herre Konung, Gud unne dig länge lefva.
Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ran sarki yă daɗe,
10 Du hafver, o Konung, låtit utgå ett bud, att alla menniskor, då de hörde ljudet af basuner, trummeter, harpor, gigor, psaltare, lutor och allahanda strängaspel, skulle de nederfalla, och tillbedja det gyldene belätet;
Ya sarki, ka fitar da doka, cewa duk wanda ya ji karar ƙaho, da sarewa, da garayu da goge, da molo da algaita da kowane irin kayan kaɗe-kaɗe da bushe-bushe sai yă rusuna yă yi sujada ga siffar zinariya,
11 Och den som icke nederfölle och tillbåde, han skulle kastas uti en brinnande ugn.
kuma cewa duk wanda bai rusuna ya yi sujadar ba za a jefa shi cikin tanderun wuta.
12 Nu äro här någre Judiske män, hvilka du öfver de ämbete i Babels land satt hafver, Sadrach, Mesach och AbedNego; de samme förakta ditt bud, o Konung, och vörda icke dina gudar, och tillbedja icke det gyldene belätet, som du hafver uppsätta låtit.
Amma sai ga waɗansu Yahudawa waɗanda ka ɗora su a kan harkokin yankin Babilon, wato, Shadrak, Meshak da Abednego waɗanda ba su kula da umarninka ba, ya sarki. Ba su bauta wa allolin ba balle su yi sujada ga gunkin zinariya da ka kafa.”
13 Då befallde NebucadNezar, med grymhet och vrede, att man skulle hafva fram för honom Sadrach, Mesach och AbedNego; och männerne vordo framhafde för Konungen.
Cikin fushi da hasala, Nebukadnezzar ya aika a kira Shadrak, Meshak da Abednego. Aka kawo waɗannan mutane a gaban sarki,
14 Då talade NebucadNezar till dem, och sade: Huru är det? Viljen I, Sadrach, Mesach och AbedNego, icke vörda min gud, och icke tillbedja det gyldene belätet, som jag hafver uppsätta låtit?
sai Nebukadnezzar ya ce musu, “Gaskiya ne Shadrak, Meshak da Abednego, cewa kun ƙi ku bauta wa alloli kuka kuma ƙi yi sujada ga gunkin da na kafa?
15 Nu väl, reder eder till, så snart I hören ljudet af basuner, trummeter, harpor, gigor, psaltare, lutor och allahanda strängaspel, så faller neder, och tillbeder belätet, som jag hafver uppsätta låtit; om I icke tillbedjen det, så skolen I på samma stund varda kastade uti en brinnande ugn. Låt se, hvilken den Guden är, som eder utu mina händer tager.
Yanzu sa’ad da kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, in kuna a shirye ku rusuna ƙasa ku yi wa wannan gunkin da na yi sujada, to, da kyau. Amma in ba ku yi sujada ba, za a je fa ku yanzu a cikin tanderun wutar nan. In ga kowane ne allahn nan da zai kuɓutar da ku daga hannuna?”
16 Då svarade Sadrach, Mesach och AbedNego, och sade till Konung NebucadNezar: Det är icke af nödene, att vi svare dig deruppå.
Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka amsa wa sarki suka ce, “Ya Nebukadnezzar, ba mu bukata mu kāre kanmu a gabanka a kan wannan batu.
17 Si, vår Gud, den vi dyrke, kan väl hjelpa oss utu den brinnande ugnen, och frälsa oss utu dine hand, o Konung.
In an jefa mu cikin tanderun wutar nan, Allahn da muke bauta wa zai iya cetonmu daga ita, kuma ya sarki, zai cece mu daga hannunka.
18 Och om han än icke det göra vill, så skall du ändå veta, o Konung, att vi dina gudar intet vörde, ej heller det gyldene beläte, som du hafver uppsätta låtit, tillbedja viljom.
Amma ko da bai cece mu ba, muna so ka sani, ya sarki; cewa ba za mu bauta wa allolinka ba ko kuma mu yi sujada ga gunkin zinariyar da ka kafa ba.”
19 Då vardt NebucadNezar full med grymhet, så att hans ansigte förvandlade sig öfver Sadrach, Mesach och AbedNego; och befallde, att man skulle göra ugnen sju resor hetare, än han eljest plägade vara;
Sai Nebukadnezzar ya husata da Shadrak, Meshak da Abednego, sai al’amuransa a kansu ya canja. Sai ya umarta a ƙara zuga wutar har sau bakwai domin tă yi zafi fiye da yadda take a dā.
20 Och böd de bästa krigsmän, som uti hans här voro, att de skulle binda Sadrach, Mesach och AbedNego, och kasta dem uti den brinnande ugnen.
Kuma ya umarci waɗansu ƙarfafan sojoji a cikin rundunarsa su daure Shadrak, Meshak da Abednego su jefa su cikin tanderun wutar.
21 Alltså vordo desse männerna, uti deras mantlar, skor, hattar och annor kläder, bundne, och kastade uti den brinnande ugnen.
Waɗannan mutanen suna sanye da riguna, da wanduna, da rawani da waɗansu kayan sawa, aka daure su, aka jefa su cikin tanderun wuta.
22 Ty Konungens befallning måste man med hast fullgöra; och elden vardt så stark i ugnen, att de män, som Sadrach, Mesach och AbedNego uppbränna skulle, blefvo döde af eldslåganom.
Sarki ya ba da umarnin da gaggawa kuma wutar ta yi zafi ƙwarai har harshen wutar ya kashe sojojin nan da suka ɗauki Shadrak, Meshak da Abednego,
23 Men de tre männerna, Sadrach, Mesach och AbedNego, föllo neder uti den brinnande ugnen, så bundne som de voro.
waɗannan mutane uku kuma a daure, suka fāɗa cikin tanderun wutar.
24 Då förskräckte sig Konung NebucadNezar, och gick hastigt upp, och sade till sitt Råd: Hafve vi icke låtit kasta tre män i elden bundna? De svarade, och sade till Konungen: Ja, Herre Konung.
Sai Sarki Nebukadnezzar ya miƙe tsaye, cike da mamaki ya tambayi mashawartansa, “Shin ba mutum uku ba ne muka daure muka jefa cikin wutar?” Suka amsa, “Tabbatacce haka yake ya sarki.”
25 Han svarade, och sade: Ser jag dock fyra män lösa gå i eldenom, och dem skadar intet; och den fjerde är lika som han vore en Gudason.
Sai ya ce, “Ku duba ina ganin mutum huɗu suna tafiya suna yawo a cikin wutar, a sake kuma babu abin da ya same su, na huɗun sai ka ce ɗan alloli.”
26 Och NebucadNezar gick fram för gapet på den brinnande ugnen, och sade: Sadrach, Mesach och AbedNego, högsta Guds tjenare, går härut, och kommer hit. Så gingo Sadrach, Mesach och AbedNego, utur eldenom.
Sai Nebukadnezzar ya matsa kusa da ƙofar tanderun wutar ya yi kira da ƙarfi, “Shedrak, Meshak da Abednego, bayin Allah Mafi Ɗaukaka ku fito! Ku zo nan!” Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka fita daga cikin wutar,
27 Och Förstarna, herrarna, fogdarna, och Konungens Råd kommo tillsamman, och sågo uppå, huru elden ingen magt uppå dessa männernas kroppar bevisat hade; och deras hufvudhår icke ens afsvedet var, och deras kläder intet skadd; ja, man kunde icke känna någon eldslukt uppå dem.
Sa’an nan hakimai, da wakilai, da gwamnoni da masu ba wa sarki shawara suka kewaya su. Suka ga wutar ba tă yi musu wani lahani a jikinsu ba, babu ko gashin kansu da ya ƙuna; ko warin wuta ma ba su yi ba.
28 Då hof NebucadNezar sin röst upp, och sade: Lofvad vare Sadrachs, Mesachs och AbedNegos Gud, den sin Ängel utsändt hafver, och halp sina tjenare, som uppå honom trodde, och icke gjorde efter Konungens bud, utan utgåfvo deras lekamen, att de ingen gud ära eller tillbedja ville, utan allena sin Gud.
Sa’an nan Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allahn Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko da mala’ikansa ya ceci bayinsa da suka dogara matuƙa a gare shi, suka ki bin umarnin sarki kuma su na a shirye domin su ba da ransu da suka ƙi bauta ko su yi sujada ga wani allah sai dai Allahnsu.
29 Så är nu detta mitt bud: Att ho som helst ibland all folk, slägter och tungomål, försmäder Sadrachs, Mesachs och AbedNegos Gud, han skall förgöras, och hans hus skamliga förstördt varda; ty det är ingen annar gud, som så hjelpa kan, som denne.
Domin haka ina ba da doka cewa duk mutane da kowace al’umma ko kowane yaren da ya ce wani abu mummuna a kan Allahn Shadrak, Meshak da Abednego za a yanka shi gunduwa-gunduwa kuma gidansu zai zama wurin zuba shara, domin babu wani allahn da zai iya ceto ta irin wannan hanya.”
30 Och Konungen gaf Sadrach, Mesach och AbedNego, stort välde i Babels land.
Sa’an nan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a yankin Babilon.