< Amos 5 >

1 Hörer, I af Israels hus, detta ordet: ty jag måste göra denna klagovisona öfver eder.
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 Jungfrun Israel är fallen, så att hon intet mer uppstå kan; hon är stött neder till jordena, och ingen är som upphjelper henne.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Ty så säger Herren Herren: Den staden, der tusende utgå, der skola icke utan hundrade qvar blifva i och der hundrade utgå, skola icke utan tio igen behållne blifva i Israels bus.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Derföre, så säger Herren till Israels hus: Söker mig, så skolen I lefva.
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 Söker icke BethEl, och kommer intet till Gilgal, och går icke till BerSeba; förty Gilgal, skall varda fånget bortfördt, och BethEl skall i jämmer komma.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Söker Herran, så skolen I lefva, på det i Josephs huse icke uppågå skall en eld, hvilken förtärer, och icke utsläckas kan uti BethEl.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 I som förvänden rätten uti malört, och stöten rättvisona neder till jordena;
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 Han gör sjustjernorna och Orion han gör af mörkret morgonen, och af dagen mörka nattena; han kallar vattnet i hafvena, och gjuter det uppå jordenes krets; han heter Herren;
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 Den der en förstöring beställer öfver den starka, och låter komma en förstöring öfver den fasta staden.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 Men de äro honom gramse, som dem uppenbara straffar, och hafva en styggelse vid den som helsosamt lärer.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Derföre, efter I undertrycken den fattiga, och tagen korn af honom i storom bördom, så skolen I icke bo uti husomen, som I af huggen sten uppbyggt hafven, och icke dricka det vin, som I uti de sköna vingårdar planterat hafven.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 Ty jag vet edor öfverträdelse, den mycken är, och edra synder, de der starka äro; huru I trängen de rättfärdiga, och tagen gåfvor, och undertrycken de fattiga i domenom.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Derföre måste den kloke tiga på den tiden; ty det är en ond tid.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Söker det goda, och icke det onda, på det I lefva mågen; så skall Herren Gud Zebaoth vara med eder, såsom I berömmen.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Hater det onda, och älsker det goda; skaffer rätt i portenom; så skall Herren Gud Zebaoth vara nådelig öfver de igenlefda i Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Derföre, så säger Herren Gud Zebaoth, Herren: Det skall varda klagogråt på alla gator, och på alla vägar skall man säga: Ack ve, ack ve! Och man skall kalla åkermannen till sorg, och till klagogråt den der gråta kan.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 Uti alla, vingårdar skall klagogråt vara; ty jag vill fara fram ibland eder, säger Herren.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Ve dem som begära Herrans dag! Hvad skall han eder? Ty Herrans dag är ett mörker, och icke ljus;
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 Lika som då någor flydde för ett lejon, och honom mötte en björn; och lika som någor in uti ett hus komme, och ledde sig med handene utmed väggene, och en orm stunge honom.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Ty Herrans dag skall ju vara mörk, och icke ljus; skum, och icke klar?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Jag är edrom högtidom gramse, och föraktar dem, och kan icke lida edart rökoffer uti edra församlingar.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 Och om I mig än offraden bränneoffer och spisoffer, så hafver jag dock ingen lust dertill; så orkar jag ock icke se edart feta tackoffer.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Haf bort dina visors buller ifrå mig; ty jag orkar icke höra ditt psaltarespel.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Men rätten skall uppenbarad varda lika som vatten, och rättvisan såsom en stark flod.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Hafven I, af Israels hus, ock offrat mig slagtoffer och spisoffer i öknene, i fyratio år långt? Ja, skönliga.
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 I bären edars Molochs hyddor, och edra afgudars beläte, och edra gudars stjerno, som eder sjelfve gjort haden.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 Så skall jag låta föra eder hädan bort till Damascus, säger Herren, som Gud Zebaoth heter.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.

< Amos 5 >