< 2 Timotheosbrevet 2 >
1 Så stärk dig nu, min son, genom nådena, som är i Christo Jesu.
Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
2 Och hvad du af mig hört hafver, genom mång vittne, det befalla trogna menniskor, som ock dugelige äro att lära andra.
Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
3 Lid och umgäll, såsom en god Jesu Christi stridsman.
Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
4 Ingen stridsman befattar sig med näringshandel; på det han skall täckas honom, som honom till en stridsman upptagit hafver.
Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
5 Hvar ock nu någor kämpar, han krönes icke, utan han redeliga kämpar.
Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
6 Åkermannen, som åkren brukar, honom bör först få af fruktene.
Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
7 Märk hvad jag säger; men Herren skall gifva dig i all ting förstånd.
Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
8 Tänk på Jesum Christum, som är uppstånden ifrå de döda, af Davids säd, efter mitt Evangelium;
Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
9 Uti hvilket jag bedröfvelse lider, intill bojor, såsom en ogerningsman; men Guds ord är icke bundet.
wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
10 Derföre lider jag det allt, för de utkoradas skull, att de skola ock få salighet i Christo Jesu, med eviga härlighet. (aiōnios )
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
11 Det är ju ett fast ord: Dö vi med, så skole vi lefva med;
Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
12 Lide vi, så skole vi med regnera; om vi försake honom, så försakar ock han oss.
in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
13 Tro vi honom icke, så blifver han dock trofast; han kan icke neka sig sjelf.
in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
14 Sådant förmana, och betyga för Herranom, att de icke träta om ord till ingen nytto, utan till att afvända dem som på höra.
Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
15 Vinnlägg dig att bevisa dig Gudi en bepröfvad och ostraffelig arbetare, som rätt delar sanningenes ord.
Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
16 Men oandelig och onyttig ord kasta bort; ty det hjelper mycket till ogudaktighet;
Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
17 Och deras tal fräter omkring sig, såsom kräfvetan; ibland hvilka är Hymeneus och Philetus;
Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
18 De der om sanningen felat hafva, sägande uppståndelsen redan skedd vara; och hafva förvändt somliga menniskors tro.
waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
19 Men den faste Guds grund blifver ståndandes, och hafver detta insegel: Herren känner sina; och hvar och en som åkallar Christi Namn, gånge ifrå orättfärdighetene.
Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
20 Men uti ett stort hus äro icke allenast gyldene och silffat, utan jemväl träfat och lerfat; och somlig till heder, och somlig till vanheder.
A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
21 Hvar nu någor renar sig ifrå sådant folk, han varder ett helgadt fat till heder, husherranom brukeligit, beredt till allt godt verk.
In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
22 Fly ungdomsens lustar; men far efter rättfärdigheten, tron, kärleken, frid med allom dem, som af rent hjerta åkalla Herran.
Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 Men förkasta dåraktig och öfverdådig spörsmål, vetandes att de föda träto af sig.
Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
24 Men Herrans tjenare skall icke vara trätosam, utan ljuflig vid hvar man, läraktig, den de onda lida kan;
Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
25 Och med saktmodighet straffa dem som emotstå; om Gud en gång vill gifva dem bättring, till att förstå sanningen;
Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
26 Och besinna sig ifrå djefvulens snaro, af hvilkom de fångne äro efter hans vilja.
su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.