< 2 Samuelsboken 15 >

1 Och det begaf sig derefter, att Absalom beställde sig vagnar och resenärar, och femtio män, som hans drabanter voro.
Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
2 Och Absalom stod bittida upp om morgonen, och gick in på den vägen vid porten; och hvar någor hade ett ärende, så att han skulle komma till rätta för Konungen, den kallade Absalom till sig, och sade: Utaf hvad stad äst du? Då nu någor sade: Din tjenare är utaf ene af Israels slägter,
Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
3 Så sade Absalom till honom: Si, din sak är god och rätt: men du hafver ingen, som dig förhörer af Konungenom.
Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
4 Och Absalom sade: Ack! ho sätter mig till domare i landena, att hvar man måtte komma till mig, den någon sak och klagan hafver, att jag måtte hjelpa honom till rätta?
Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
5 Och när någon gick fram till honom, till att tala med honom, så räckte han sina hand ut, och fick honom fatt, och kysste honom.
Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
6 Vid det sättet gjorde Absalom allom Israel, när de kommo med några saker till Konungen; och stal alltså bort männernas hjerta af Israel.
Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
7 Efter fyratio år sade Absalom till Konungen: Jag vill gå bort och fullkomna mitt löfte i Hebron, som jag Herranom lofvat hafver.
A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
8 Förty din tjenare gjorde ett löfte, då jag bodde i Gesur i Syrien, och sade: När Herren låter mig återkomma till Jerusalem, så vill jag göra Herranom en Gudstjenst.
Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
9 Konungen sade till honom: Gack i frid. Och han stod upp, och gick till Hebron.
Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
10 Men Absalom hade utsändt spejare uti alla Israels slägter, och lät säga: När I fån höra ljudet af basunen, så säger: Absalom är Konung vorden i Hebron.
Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
11 Och med Absalom gingo tuhundrad män af Jerusalem kallade; men de gingo i enfaldighet, och visste intet af sakene.
Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
12 Sände ock desslikes Absalom efter Achitophel den Giloniten, Davids rådgifvare, utaf hans stad Gilo; och som han nu hade offrat, vardt förbundet starkt, och folket lopp till, och förökades med Absalom.
Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
13 Så kom en och bidade David, och sade: Hvars mans hjerta i Israel följer Absalom efter.
Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
14 Men David sade till alla sina tjenare, som när honom voro i Jerusalem: Upp, låt oss fly; ty här blifver ingen undflykt för Absalom; skynder eder, låt oss gå, att han icke är snarare än vi, och får oss fatt, och drifver inuppå oss det ondt är, och slår staden med svärdsegg.
Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
15 Då sade Konungens tjenare till honom: Hvad min herre Konungen täckes, si, här äro dine tjenare.
Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
16 Och Konungen gick ut till fot, med allt sitt hus; men han lät blifva qvara tio frillor, till att bevara huset.
Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
17 Och då Konungen och allt folket till fot utkommo, gingo de bortåt långt ifrå huset.
Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
18 Och alle hans tjenare gingo när honom; dertill alle Crethi och Plethi, och alle de Gitthiter; sexhundrad män, som af Gath till fot komne voro, gingo framför Konungenom.
Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
19 Och Konungen sade till Itthai den Gitthiten: Hvi går du ock med oss? Vänd om, och blif när Konungenom; ty du äst främmande; far ock igen till ditt rum.
Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
20 I går komst du, och i dag vågar du dig till att gå med oss? Jag går hvart jag gå kan, vänd om, och dina bröder med; dig vederfare barmhertighet och trohet.
Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
21 Itthai svarade, och sade: Så sant som Herren lefver, och så sant som min herre Konungen lefver, hvar som helst min herre Konungen blifver, antingen i lifvet eller i döden, der skall din tjenare ock blifva.
Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
22 David sade till Itthai: Så kom, och gack med. Alltså gick Itthai den Gitthiten, och alle hans män, och hela barnahopen, som med honom var.
Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
23 Och hela landet greto med höga röst, och allt folket gick med; och Konungen gick öfver den bäcken Kidron, och allt folket gick före, på den vägen som löper åt öknena.
Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
24 Och si, Zadok var ock der, och alle Leviterna, som med honom voro, och båro Gudsförbunds ark, och der satte de honom; och AbJathar steg upp, tilldess allt folket kom utu stadenom.
Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
25 Men Konungen sade till Zadok: Bär Guds ark åter in i staden; om jag finner nåd för Herranom, så låter han mig väl komma igen, och låter mig få se honom, och sitt hus.
Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
26 Men om han säger: Jag hafver intet behag till dig; si, här är jag; han göre med mig såsom honom täckes.
Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
27 Och Konungen sade till Presten Zadok: O Siare, vänd om igen i staden med frid; och med eder Ahimaaz din son, och Jonathan, AbJathars son.
Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
28 Si, jag vill draga fram på slättmarkena i öknene, tilldess bådskap kommer ifrån eder, och gifver mig all ting tillkänna.
Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
29 Så båro då Zadok och AbJathar Guds ark in i Jerusalem igen, och blefvo der.
Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
30 Men David gick uppfor oljoberget, och gret, och hans hufvud var skyldt, och han gick barfött; dertill allt folket, som med honom var, hade hvar och en förskylt sitt hufvud, och gingo uppåt gråtandes.
Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
31 Och då David vardt sagdt, att Achitohel var i förbundet med Absalom, sade han: Herre, gör Achitophels rådslag till galenskap.
To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
32 Och då David kom öfverst på berget, der man plägar tillbedja Gud; si, der mötte honom Husai, den Architen, med sönderrifven kjortel, och jord på hans hufvud.
Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
33 Och David sade till honom: Om du går med mig, äst du mig till tunga.
Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
34 Men går du åter i staden, och säger till Absalom: Jag är din tjenare, jag vill höra Konungenom till; jag, som tillförene var dins faders tjenare, vill nu vara din tjenare; så kan du göra Achitophels rådslag om intet.
Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
35 Och äro der Zadok och AbJathar Presterna med dig; allt det du hörer utu Konungens hus, må du undervisa Presterna Zadok och AbJathar.
Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
36 Och si, när dem äro två deras söner, Ahimaaz, Zadoks, och Jonathan, AbJathars son, genom dem kan du bjuda mig till hvad du förnimmer.
’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
37 Så kom då Husai, Davids vän, i staden, och Absalom kom till Jerusalem.
Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.

< 2 Samuelsboken 15 >