< 2 Kungaboken 13 >

1 Uti tredje och tjugonde årena Joas, Ahasia sons, Juda Konungs, vardt Joahas, Jehu son, Konung öfver Israel i Samarien, sjutton år.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 Och han gjorde det ondt var för Herranom, och vandrade efter Jerobeams synder, Nebats sons, hvilken Israel kom till att synda; och öfvergaf det icke.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 Och Herrans vrede förgrymmade sig öfver Israel, och gaf dem under Hasaels hand, Konungens i Syrien, och i Benhadads, Hasaels sons, hand, i deras lifsdagar.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Men Joahas bad Herrans ansigte, och Herren hörde honom; ty han såg på Israels jämmer, som Konungen i Syrien dem gjorde.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 Och Herren gaf Israel en frälsare, som dem förde utu de Syrers våld; så att Israels barn bodde uti sina hyddor, såsom tillförene.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Dock öfvergåfvo de icke Jerobeams hus synder, hvilken Israel kom till att synda, utan vandrade derutinnan; och den lunden i Samarien blef ståndandes.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Förty af Joahas folk var icke mer qvart blifvet, än femtio resenärer, tio vagnar, och tiotusend fotfolk; ty Konungen i Syrien hade slagit dem ihjäl, och gjort dem såsom tröskestoft.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Hvad nu mer af Joahas sägandes är, och allt det han gjort hafver, och hans magt, si, det är skrifvet i Israels Konungars Chrönico.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 Och Joahas afsomnade med sina fäder, och man begrof honom i Samarien; och hans son Joas vardt Konung i hans stad.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Uti sjunde och tretionde årena Joas, Juda Konungs, vardt Joas, Joahas son, Konung öfver Israel i Samarien, sexton år;
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 Och gjorde det ondt var för Herranom, och öfvergaf icke alla Jerobeams, Nebats sons, synder, den Israel kom till att synda; utan vandrade derutinnan.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 Hvad nu mer af Joas sägandes är, och hvad han gjort hafver, och hans magt, huru han med Amazia, Juda Konung, stridt hafver, si, det är skrifvet uti Israels Konungars Chrönico.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 Och Joas afsomnade med sina fader; och Jerobeam satt på hans stol. Men Joas vardt begrafven i Samarien när de Israels Konungar.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Då vardt Elisa krank, der han ock af död blef; och Joas, Israels Konung, kom ned till honom, och gret för honom, och sade: Min fader, min fader, Israels vagn, och hans resenärer.
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Elisa sade till honom: Tag bågan och pilarna. Och då han tog bågan och pilarna,
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Sade han till Israels Konung: Bänd bågan med dine hand. Och han bände med sine hand. Och Elisa lade sina hand på Konungens hand;
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Och sade: Låt upp fenstret österut; och han lät det upp. Och Elisa sade: Skjut; och han sköt. Han sade: En salighetspil af Herranom, en salighetspil emot de Syrer; och du skall slå de Syrer i Aphek, tilldess de blifva ändade.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Och han sade: Tag pilarna. Och då han tog dem, sade han till Israels Konung: Slå på jordena. Och han slog tre gånger, och höll upp.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Då vardt Guds mannen vred på honom, och sade: Hade du slagit fem eller sex gånger, så skulle du hafva slagit de Syrer, tilldess du hade gjort en ända på dem; men nu skall du slå dem tre gånger.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Då nu Elisa var död, och man hade begrafvit honom, föllo de Moabiters krigsfolk in uti landet på samma året.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 Och det begaf sig, att de begrofvo en man; och som de fingo se krigsfolket, kastade de mannen uti Elisa graf; och då han kom vid Elisa ben, vardt han lefvandes, och stod upp på sina fötter.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Alltså tvingade nu Hasael, Konungen i Syrien, Israel, så länge Joahas lefde.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 Men Herren gjorde nåd med dem, och förbarmade sig öfver dem, och vände sig till dem för sitt förbunds skull med Abraham, Isaac och Jacob, och ville, icke förderfva dem; och förkastade dem icke heller ifrå sitt ansigte allt härtill.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Och Hasael, Konungen i Syrien, blef död; och hans son Benhadad vardt Konung i hans stad.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Men Joas vände om, och tog de städer igen utu Benhadads, Hasaels sons, hand, som han utu hans faders Joahas hand med strid tagit hade. Tre gånger slog Joas honom, och fick Israels städer igen.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kungaboken 13 >