< 1 Samuelsboken 8 >

1 Då nu Samuel vardt gammal, satte han sina söner till domare öfver Israel.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 Hans förstfödde son het Joel, och den andre Abia; och de voro domare i BerSaba.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 Men hans söner vandrade icke uti hans vägar; utan böjde sig efter girighet, och togo gåfvor, och förvände rätten.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Så församlade sig alle äldste i Israel, och kommo till Ramath till Samuel;
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 Och sade till honom: Si, du äst vorden gammal, och dine söner gå icke uti dina vägar: så sätt nu en Konung öfver oss, den oss döma må, såsom alle Hedningar hafva.
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 Det behagade Samuel illa, när de sade: Få oss en Konung, den oss döma må. Och Samuel bad inför Herranom.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 Och Herren sade till Samuel: Hör folkens röst i allt det de hafva talat dig till; förty de hafva icke förkastat dig, utan mig, att jag icke skall vara Konung öfver dem.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 De göra dig såsom de alltid gjort hafva, ifrå den dag, då jag förde dem utur Egypten, allt intill denna dag; och hafva öfvergifvit mig, och tjent andra gudar.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 Så hör nu deras röst; dock betyga dem, och undervisa dem Konungens rätt, den öfver dem råda skall.
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 Och Samuel sade all Herrans ord folkena, som af honom Konung begärat hade.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 Detta skall vara Konungs rätt, den öfver eder råda skall; edra söner skall han taga till sin vagn, och resenärar som rida för hans vagn;
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 Och till höfvitsmän öfver tusende, och öfver femtio, och till åkermän, som hans åker bruka skola, och till uppskärare i hans säd, och de som göra hans harnesk, och det hans vagnar tillhörer.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 Edra döttrar skall han taga sig till apothekerskor, kokerskor och bakerskor.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 Edra bästa åkrar och vingårdar, och oljogårdar skall han taga och gifva sina tjenare;
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 Dertill skall han taga af edra säd och vingårdar tiond, och gifva sina kamererare och tjenare;
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 Och edra tjenare och tjenarinnor, och edra dägeligaste ynglingar, och edra åsnar, skall han taga, och uträtta sin ärende med.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 Af edra hjordar skall han taga tiond; och I måsten vara hans trälar.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 När I då ropen på den tiden öfver edar Konung, som I eder utvalt hafven, så skall Herren på den tiden intet höra eder.
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 Men folket ville intet höra Samuels röst, och sade: Ingalunda, utan en Konung måste vara öfver oss;
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 Att vi ock äre såsom alle andre Hedningar; att vår Konung må döma oss, och draga ut för oss, när vi före vårt örlig.
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 Så hörde Samuel allt detta, som folket sade: och sade det för Herrans öron.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 Och Herren sade till Samuel: Hör deras röst, och gör dem en Konung. Och Samuel sade till Israels män: Går edra färde, hvar och en i sin stad.
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuelsboken 8 >