< 1 Samuelsboken 15 >

1 Men Samuel sade till Saul: Herren sände mig, att jag skulle smörja dig till Konung öfver hans folk Israel; så hör nu röstena af Herrans ord.
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ni ne wanda Ubangiji ya aika in shafe ka ka zama sarki bisa mutanensa Isra’ila. Saurara yanzu ka ji saƙo daga wurin Ubangiji.
2 Så säger Herren Zebaoth: Jag hafver tänkt uppå hvad Amalek gjorde Israel, och huru han låg i vägen för honom, då han drog utur Egypten.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan hori Amalekawa saboda abin da suka yi wa Isra’ila sa’ad da suka ba su wahala yayinda suka fito daga Masar.
3 Så drag nu åstad, och slå de Amalekiter, och gif dem tillspillo med allt det de hafva; skona dem intet, utan dräp både man och qvinno, barn, och dem som dia, fä och får, camel och åsna.
Yanzu ka tafi ka yaƙi Amalekawa, ka hallaka kome da yake nasu, kada ka bar su da rai, ka kashe maza, da mata, da yara, da jarirai, da dabbobi, da tumaki, da raƙuma, da kuma jakuna.’”
4 Saul lät detta komma för folket, och talde dem i Telaim, tuhundradtusend fotfolk, och tiotusend män af Juda.
Sai Shawulu ya tattara sojoji, ya ƙidaya su a Telayim, ya sami su dubu ɗari biyu da dubu goma daga Yahuda.
5 Och då Saul kom till de Amalekiters stad, satte han ett bakhåll vid bäcken;
Shawulu ya tafi birnin Amalek ya yi kwanto a kwari.
6 Och lät säga de Keniter: Går edra färde, och gifver eder ifrå de Amalekiter, att jag icke utrotar eder med dem; förty I gjorden barmhertighet med all Israels barn, då de drogo utur Egypten. Alltså gåfvo de Keniter sig ifrå de Amalekiter.
Sai Shawulu ya ce wa Keniyawa, “Ku tashi ku bar Amalekawa don kada in hallaka ku tare da su, saboda kun yi wa dukan Isra’ilawa kirki, lokacin da suka fito daga Masar.” Saboda haka Keniyawa suka tashi suka bar Amalekawa.
7 Då slog Saul de Amalekiter, allt ifrå Hevila intill Sur, som ligger för Egypten;
Sa’an nan Shawulu ya ci Amalekawa da yaƙi tun daga Hawila har zuwa Shur, a gabashin iyakar Masar.
8 Och grep Agag, de Amalekiters Konung, lefvande; och allt folket gaf han tillspillo med svärdsegg.
Ya kama Agag sarkin Amalekawa da rai. Ya kuma hallaka dukan mutanensa da takobi.
9 Men Saul och folket skonade Agag, och hvad god får och fä var, och väl fett, och lamb, och allt det godt var, och ville icke låtat tillspillo; men det som slemt var, och intet dogde, det läto de tillspillo.
Amma Shawulu da sojojinsa suka bar Agag, da tumaki, da shanu, da’yan maruƙa masu ƙiba da kuma duk abin da yake mai kyau da rai. Waɗannan ba su so su hallaka su gaba ɗaya ba, amma duk abin da ba a so da kuma marar amfani suka hallaka.
10 Då skedde Herrans ord till Samuel, och sade:
Sai Ubangiji ya yi magana da Sama’ila ya ce,
11 Mig ångrar, att jag hafver gjort Saul till Konung; ty han hafver vändt sig ifrå mig, och icke fullkomnat min ord. Dess vardt Samuel vred; och ropade till Herran den hela nattena.
“Na damu da na naɗa Shawulu sarki, domin ya juya mini baya, bai kuma bi umarnina ba.” Sama’ila ya damu ƙwarai, ya yi kuka ga Ubangiji dukan dare.
12 Och Samuel stod bittida upp, att han skulle om morgonen möta Saul; och honom vardt sagdt, att Saul var kommen till Carmel, och reste sig upp ett segertecken, och var omkringdragen, och kommen neder till Gilgal.
Kashegari da sassafe sai Sama’ila ya tashi ya tafi domin yă sadu da Shawulu, amma aka gaya masa cewa Shawulu ya tafi Karmel. A can ya yi wa kansa abin tunawa don yă girmama kansa, daga can kuma ya juya ya gangara zuwa Gilgal.
13 Som nu Samuel kom till Saul, sade Saul till honom: Välsignad vare du Herranom! Jag hafver fullkomnat Herrans ord.
Da Sama’ila ya kai wurinsa, sai Shawulu ya ce, “Ubangiji yă albarkace ka, na aikata umarnin Ubangiji.”
14 Samuel svarade: Hvad är då det rop af får i min öron, och det rop af fä, som jag hörer?
Amma Sama’ila ya ce, “Ashe, waɗannan ba kukan tumaki ke nan nake ji a kunnena ba? Wane kuka shanu ke nan nake ji?”
15 Saul sade: Utaf de Amalekiter hafva de tagit det; förty folket skonade det bästa får och fä, för Herrans dins Guds offers skull; det andra hafve vi låtit tillspillo.
Shawulu ya amsa ya ce, “Sojoji ne suka kawo su daga Amalekawa. Sun bar tumaki da shanu masu kyau da rai don su yi wa Ubangiji Allahnka hadaya, amma sauran mun hallaka duka.”
16 Men Samuel svarade Saul: Städ till, att jag säger dig, hvad Herren hafver talat med mig i denna natt. Han sade: Säg.
Sama’ila ya ce, “Dakata, bari in faɗa maka abin da Ubangiji ya ce mini jiya da dare.” Shawulu ya ce, “Gaya mini.”
17 Samuel sade: Är det icke så, då du liten vast för din ögon, vardt du ett hufvud i Israels slägter, och Herren smorde dig till Konung öfver Israel?
Sama’ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra’ila ba? Ubangiji ya shafe ka ka zama sarkin Isra’ila.
18 Och Herren sände dig på vägen, och sade: Far bort, och förgör de syndare, de Amalekiter, och strid emot dem, tilldess du gör en ända på dem.
Shi kuma ya aika, ya umarce ka cewa, ‘Tafi ka hallaka Amalekawa mugayen mutanen nan duka, ka yaƙe su sai ka share su ƙaf.’
19 Hvi hafver du icke lydt Herrans röst; utan vändt dig till rof, och illa handlat inför Herrans ögon?
Me ya sa ba ka bi umarnin Ubangiji ba? Me ya sa ka sa hannu a ganima, ka kuma yi mugun abu a gaban Ubangiji?”
20 Då sade Saul till Samuel: Hafver jag dock lydt Herrans röst, och hafver dragit den vägen, som Herren mig sändt hafver; jag hafver fört hit Agag, de Amalekiters Konung, och förgjort de Amalekiter.
Shawulu ya ce, “Amma na bi umarnin Ubangiji. Na bi saƙon da Ubangiji ya ba ni. Na hallaka Amalekawa, na kuma kamo Agag sarkinsu.
21 Men folket hafver tagit af rofvet får och fä, det bästa af de spillgifno, till att offra det Herranom dinom Gud i Gilgal.
Sojoji suka kawo tumaki da shanu mafi kyau daga cikin ganimar domin a miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.”
22 Men Samuel sade: Menar du att Herren hafver lust till offer och bränneoffer, såsom dertill, att man lyder Herrans röst? Si, lydnad är bättre än offer, och höra till är bättre än det feta af vädrar.
Amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji yana murna da sadaka da hadaya fiye da biyayya ga maganar Ubangiji? Yin biyayya ta fi hadaya a kula kuma ta fi ƙibabbun raguna.
23 Förty olydnad är en trolldomssynd, och gensträfvighet är ett afguderi och afgudadyrkan; så, efter du hafver förkastat Herrans ord, hafver han ock förkastat dig; att du icke skall vara Konung.
Gama tawaye yana kama da zunubi na duba, girman kai kuma yana kama da bautar gumaka. Saboda ka ƙi maganar Ubangiji, shi ma ya ƙi ka da zaman sarki.”
24 Då sade Saul till Samuel: Jag hafver syndat, att jag hafver öfvergångit Herrans befallning och din ord; ty jag fruktade folket, och hörde deras röst.
Sai Shawulu ya ce wa Sama’ila, “Na yi zunubi, na ƙi bin umarnin Ubangiji, na kuma ƙi bin maganarka. Na ji tsoron mutane ne shi ya sa na bi maganarsu.
25 Och nu förlåt mig den synden, och vänd tillbaka med mig, att jag må tillbedja Herran.
Yanzu fa, ina roƙonka ka yafe mini zunubina, ka koma tare da ni, domin in yi wa Ubangiji sujada.”
26 Samuel sade till Saul: Jag vänder intet om med dig; ty du hafver förkastat Herrans ord, och Herren hafver ock förkastat dig, att du icke skall vara Konung öfver Israel.
Amma Sama’ila ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba. Ka ƙi maganar Ubangiji, Ubangiji kuma ya ƙi ka da zama sarki a bisa Isra’ila.”
27 Och som Samuel vände sig om, till att gå sina färde, fattade han honom i hans kjortels flik, och hon refs sönder.
Da Sama’ila ya juya zai tafi, sai Shawulu ya kama bakin rigarsa, sai rigar ta yage.
28 Då sade Samuel till honom: Herren hafver i denna dag rifvit Israels Konungarike ifrå dig, och gifvit dinom nästa, den bättre är än du.
Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji ya yage masarautar Isra’ila daga gare ka yau, ya ba wa wani daga cikin maƙwabtanka wanda ya fi ka.
29 Ljuger icke heller Hjelten i Israel, eller låter sig ångra; ty han är ingen menniska, att han sig något ångra låter.
Shi wanda yake Ɗaukakar Isra’ila ba ya ƙarya ko yă canja zuciyarsa, gama shi ba mutum ba ne da zai canja zuciyarsa.”
30 Men han sade: Jag hafver syndat; så gör mig dock du den ärona inför de äldsta af mitt folk, och för Israel, och vänd om med mig, att jag må tillbedja Herran din Gud.
Shawulu ya ce, “Na yi zunubi. Amma ina roƙonka ka ba ni girma a gaban dattawan mutanena da kuma a gaban Isra’ila, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji Allahnka sujada.”
31 Så vände då Samuel om, och följde Saul, så att Saul tillbad Herran.
Saboda haka sai Sama’ila ya koma tare da Shawulu, Shawulu kuwa ya yi wa Ubangiji sujada.
32 Och Samuel sade: Låt komma fram för mig Agag, de Amalekiters Konung; och Agag gick dristeliga fram till honom. Och Agag sade: Alltså måste man fördrifva dödsens bitterhet.
Sa’an nan Sama’ila ya ce, “Kawo mini Agag sarkin Amalekawa.” Agag kuwa ya zo wurinsa daure da sarƙa, yana tunani cewa, “Tabbatacce zancen mutuwa dai ya wuce.”
33 Samuel sade: Såsom ditt svärd hafver gjort qvinnor barnlös, så skall ock din moder blifva barnlös ibland qvinnor. Så högg Samuel Agag i stycker inför Herranom i Gilgal.
Amma Sama’ila ya ce, “Yadda takobinka ya sa mata suka rasa’ya’ya, haka mahaifiyarka za tă zama marar’ya’ya a cikin mata.” Sama’ila kuwa ya kashe Agag a Gilgal a gaban Ubangiji.
34 Och Samuel gick bort till Ramath; men Saul drog upp till sitt hus i Gibea Sauls.
Sai Sama’ila ya tafi Rama, amma Shawulu ya haura zuwa gidansa a Gibeya na Shawulu.
35 Och Samuel såg Saul intet mer intilldess han blef död; dock likväl sörjde Samuel för Sauls skull, att Herren hade ångrat sig, att han hade gjort honom till Konung öfver Israel.
Daga wannan rana Sama’ila bai ƙara saduwa da sarki Shawulu ba, har rasuwar Sama’ila, amma ya yi baƙin ciki sosai a kan Shawulu. Ubangiji kuwa ya damu da ya sa Shawulu ya zama Sarkin Isra’ila ba.

< 1 Samuelsboken 15 >