< 1 Petrusbrevet 3 >
1 Sammalunda hustrurna, vare sina män underdåniga; på det ock de, som icke tro på ordet, måga af hustrurnas umgängelse, utan ord, blifva vunne;
Haka ku kuma da kuke matan aure, kuyi biyayya da na ku mazajen, domin in har wadansunsu basa biyayya da maganar Allah, halin matansu ya shawo kansu ba tare da magana ba,
2 När de förmärka edor kyska umgängelse med fruktan.
Domin sun ga tsattsakan halinku da ladabinku.
3 Hvilkas prydning icke skall vara utvärtes, med flätadt hår, eller kringhängande guld, eller i kostelig kläder;
Haka ma adonku kar ya zama na kwalliyar waje kitson kai, kayan zinariya ko tufafi masu kawa.
4 Utan om den fördolda menniskan i hjertat är utan vank, med saktmodigom och stillom anda, det är kosteligit för Gudi.
Amma bari adon ya zama na mutum na cikin zuciya, kuma adon ya zama kyan nan marar dushewa, na kamun kai da natsatsen ruhu, wanda yake da daraja a gaban Allah.
5 Ty i så måtto hafva ock de helga qvinnor fordom prydt sig, de der satte sitt hopp till Gud, och voro sina män underdåniga.
Haka tsarkakan mata su ka yi ado kamar haka. Suka dogara ga Allah suka yi biyayya ga mazajensu.
6 Såsom Sara var lydig Abrahe, kallandes honom herra; hvilkens döttrar I vordna ären, om I väl gören, och ären icke så förfärade.
Ta haka Saratu ta yi biyayya ga Ibrahim ta kira shi “ubangiji”. Yanzu ku 'ya'yantane in dai kun yi aiki nagari, idan kuma ba ku ji tsoron wahala ba.
7 Sammaledes I män, bor när dem med förnuft, och gifver det qvinliga kärilet, såsom det der svagast är, sina äro; såsom ock medarfvingom till lifsens nåd; på det edra böner icke blifva förhindrade.
Kamar yadda na fada wa matan aure haka ma mazaje, ku zauna da mata da sanin su raunana ne abokan tarayya ne na karbar baiwar rayuwa. Ku dinga yin haka domin a rika jin addu'oinku.
8 Men på sistone, varer alle vid ett sinne, medlidande, broderlig kärlek hafvande till hvarannan, barmhertige, vänlige;
Daga karshe, dukanku ku hada hankulanku, ku zama masu juyayi, masu kauna kamar 'yan'uwa, masu taushin zuciya, masu tawali'u.
9 Icke vedergällande ondt för ondt, icke bannor för bannor; utan heldre tvärtemot, välsigner; vetandes att I ären dertill kallade, att I skolen ärfva välsignelse.
Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi. A maimakon haka ku cigaba da sa albarka, gama sabili da haka ne musamman aka kiraye ku, domin ku gaji albarka.
10 Ty den der vill älska lifvet, och se goda dagar, han stille sina tungo ifrå det ondt är, och sina läppar, att de icke tala bedrägeri;
“Wanda duk yake so ya more a rayuwarsa ya kuma ga kwanaki masu alheri, to fa, ya kame harshen sa daga mugunta da lebensa daga maganganun yaudara.
11 Vände sig ifrå det ondt är, och göre det godt är; söke efter friden, och fare honom efter.
Ya rabu da mugunta ya aikata abin da ke nagari. Bari ya nemi zaman salama ya kuma dimanceta.
12 Ty Herrans ögon äro öfver de rättfärdiga, och hans öron till deras bön; men Herrans ansigte är öfver dem som ondt göra.
Idanun Ubangiji suna duban adalai, kunnuwansa kuma suna sauraron roke rokensu. Amma fuskar Ubangiji tana gaba da masu aikata mugunta.”
13 Och ho är den som kan göra eder skada, om I faren efter det goda?
Wanene ya isa ya cuce ku idan kun himmatu ga yin abin da ke nagari?
14 Ja, om I än något liden för rättfärdighetenes skull, ären I dock likväl salige. Frukter eder intet för deras trug; icke heller förskräcker eder;
Amma idan kuna shan wuya saboda adalci, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoron abin da su ke tsoro. Kada ku damu.
15 Utan helger Herran Gud uti edor hjerta. Varer ock alltid redebogne till att svara hvarjom och enom, som begärar skäl till det hopp som i eder är; och det med saktmodighet och fruktan.
Maimakon haka, ku kebe Ubangiji a cikin zukatanku cewa shi mai tsarki ne. Kullum ku zauna da shiri domin ku amsa wa mai tambayar ku dalilin sa begenku ga Allah. Amma fa kuyi haka tare da tawali'u da bangirma.
16 Och hafver ett godt samvet; på det de, som vilja förtala eder såsom ogerningsmän, skola komma på skam, att de förlastat hafva edor goda umgängelse i Christo.
Ku zama da tsatsakan lamiri domin mutanen da ke zargin rayuwarku mai kyau cikin Almasihu, su ji kunya domin suna maganar gaba da ku kamar ku mugaye ne.
17 Ty det är bättre, om Guds vilje så är, att I för goda gerningar liden, än för onda.
Ya fi kyau, a sha wuya akan aiki nagari, idan nufin Allah ne, da a sha wuya sabili da mugun aiki.
18 Ty Christus led ock ena reso för syndernas skull, rättfärdig för orättfärdiga; på det han skulle offra oss Gudi, och är dödad efter köttet; men lefvande gjord efter Andan.
Almasihu ya sha wahala sau daya tak sabili da zunubai. Shi da ya ke mai adalci ya sha wahala domin mu marasa adalci, domin ya kawo mu ga Allah. Aka kashe shi cikin jiki, amma aka rayar da shi cikin Ruhu.
19 I dem samma gick han ock bort, och predikade för andarna i fängelset;
A Ruhu ne, ya je ya yi wa'azi ga ruhohin da ke a yanzu cikin kurkuku.
20 Som fordom icke trodde, när Gud en gång bidde, och tålamod hade i Noe tid, då arken byggdes, i hvilkom få, det är, åtta själar, blefvo frälste genom vattnet;
Sun yi rashin biyayya ne sa'adda hakurin Allah yake jiransu a lokacin Nuhu a zamanin sassaka jirgin ruwa, sai Allah ya tsirar da mutane kalilan wato rayuka takwas daga cikin ruwa.
21 Hvilket nu ock oss saliga gör i dopet, som genom hint betydt är (icke att köttsens smittor afläggas, utan att man hafver ett godt samvet till Gud), genom Jesu Christi uppståndelse;
Wannan kwatancin baftismar da take cetonmu yanzu ne, ba kamar ta wanke Dauda daga jiki ba, sai dai ta rokon Allah da lamiri mai kyau ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
22 Hvilken är på Guds högra hand, uppfaren till himla; och honom äro Änglarna, och väldigheterna, och krafterna underdåniga.
Ya hau sama. Yana dama ga Allah. Mala'iku, da mulkoki da masu iko dole su yi masa biyayya.