< 1 Kungaboken 3 >

1 Och Salomo befryndade sig med Pharao, Konungenom i Egypten, och tog Pharaos dotter, och förde henne uti Davids stad, tilldess han skulle fullbygga sitt hus, och Herrans hus, och muren omkring Jerusalem.
Solomon ya haɗa kai da Fir’auna sarkin Masar, ya kuwa auri’yarsa. Ya kawo ta cikin Birnin Dawuda kafin yă gama ginin fadarsa, da haikalin Ubangiji, da kuma katanga kewaye da Urushalima.
2 Men folket offrade ännu på höjdomen; ty det var ändå intet hus bygdt Herrans Namne, intill den tiden.
A lokacin dai mutane suna miƙa hadaya a wurare a bisa tuddai, domin ba a riga an gina haikali saboda Sunan Ubangiji ba.
3 Men Salomo hade Herran kär, och vandrade efter sins faders Davids seder; undantagno att han offrade, och rökte uppå höjdomen.
Solomon ya ƙaunaci Ubangiji ta wurin yin tafiya bisa ga farillan mahaifinsa Dawuda, sai dai ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a wuraren nan na bisa tuddai.
4 Och Konungen gick bort till Gibeon, till att offra der; ty der var en härlig höjd; och Salomo offrade tusende bränneoffer på det samma altaret.
Sai sarki Solomon ya tafi Gibeyon don yă miƙa hadayu, gama a can ne wuri mafi muhimmanci na sujada. Solomon kuwa ya miƙa hadayun ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade.
5 Och Herren syntes Salomo i Gibeon, uti en dröm om nattene. Och Gud sade: Bed hvad jag skall gifva dig.
A Gibeyon, Ubangiji ya bayyana ga Solomon da dare a mafarki, Allah ya ce, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.”
6 Salomo sade: Du hafver gjort med min fader David din tjenare stora barmhertighet, såsom han vandrade för dig i sanning och rättfärdighet, och med ett rättsinnigt hjerta när dig; och du hafver hållit honom denna stora barmhertigheten, och gifvit honom en son, som på hans stol sitta skulle, såsom nu tillgår.
Solomon ya amsa ya ce, “Ka nuna alheri mai girma ga bawanka, mahaifina Dawuda domin ya yi aminci gare ka da adalci, ya kuma kasance da zuciya mai gaskiya. Ka ci gaba da wannan alheri mai girma gare shi, ka ba shi ɗa don yă zauna a kujerar sarautarsa a wannan rana.
7 Nu, Herre min Gud, du hafver gjort din tjenare till Konung i mins faders Davids stad; så är jag en ung dräng, och vet icke min utgång eller ingång.
“Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka sa bawanka a wurin mahaifina Dawuda. Amma ni ɗan yaro ne kawai, ban kuma san yadda zan yi ayyukana ba.
8 Och din tjenare är ibland ditt folk, som du utvalt hafver, det så mycket är, att det ingen räkna eller beskrifva kan, för myckenhets skull.
Bawanka yana nan a cikin mutanen da ka zaɓa, mutane masu girma, waɗanda suka wuce ƙirge, ko a lissafta.
9 Så gif nu dinom tjenare ett lydaktigt hjerta, att han må döma ditt folk, och förstå hvad godt och ondt är; ty ho förmår döma detta ditt mägtiga folk?
Saboda haka ka ba bawanka zuciyar ganewa, don yă shugabanci mutanenka, yă kuma iya rarrabe tsakanin abin da yake daidai da abin da ba daidai ba. Gama wa zai iya shugabance wannan mutanenka masu girma haka?”
10 Då täcktes det Herranom väl, att Salomo bad om sådant.
Sai Ubangiji ya ji daɗi cewa Solomon ya roƙa wannan.
11 Och Gud sade till honom: Efter du detta beddes, och bad icke om långt lif eller rikedomar, eller om dina fiendars själar, utan om förstånd till att döma,
Saboda haka Allah ya ce masa, “Da yake ka nemi wannan ne, ba ka kuwa nemi tsawon rai ko arziki wa kanka ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, amma ka nemi ganewa a aikata gaskiya,
12 Si, så hafver jag gjort efter din ord; si, jag hafver gifvit dig ett vist och förståndigt hjerta, så att din like hafver icke varit för dig, och icke heller efter dig uppkomma skall.
zan yi abin da ka roƙa. Zan ba ka zuciya mai hikima da ta ganewa, har yă zama ba a taɓa samun wani kamar ka ba, ba kuwa za a taɓa samunsa ba.
13 Dertill det du icke bedit hafver, det hafver jag också gifvit dig, nämliga rikedomar och härlighet; så att ingen skall vara din like ibland Konungarna i dina dagar.
Ban da haka ma, zan ba ka abin da ba ka nema ba; arziki da girma, don a rayuwarka ba za ka kasance da wani kamar ka ba a cikin sarakuna.
14 Och om du vandrar i mina vägar, så att du håller mina seder och bud, såsom din fader David vandrat hafver, så vill jag gifva dig långt lif.
In kuma ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi biyayya da farillaina da umarnaina kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, zan ba ka tsawon rai.”
15 Och då Salomo vaknade, si, då var det en dröm; och han kom till Jerusalem, och gick fram för Herrans förbunds ark, och offrade bränneoffer och tackoffer; och gjorde ett stort gästabåd allom sinom tjenarom.
Sai Solomon ya farka, ya gane ashe mafarki ne. Ya koma Urushalima, ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji ya miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama. Sa’an nan ya shirya wa fadawansa biki.
16 På den tiden kommo två skökor för Konungen, och gingo fram för honom.
To, ana nan sai waɗansu karuwai biyu suka zo wurin sarki, suka tsaya a gabansa.
17 Och den ena qvinnan sade: Ack! min Herre, jag och denna qvinnan bodde uti ett hus, och jag födde när henne i huset.
Sai ɗaya ta ce, “Ranka yă daɗe, wannan mata da ni muna zama a gida ɗaya. Na haifi jariri yayinda take can tare da ni.
18 Och efter tre dagar, sedan jag födt hade, födde hon och; och vi voro tillhopa, så att ingen främmande var med oss i huset, utan vi båda.
Kwana uku bayan haihuwar jaririna, wannan mata ma ta haifi jariri. Mu dai kaɗai ne; babu wani a gidan sai mu biyu.
19 Och denna qvinnones son blef död om nattena; ty hon förkramade honom i sömnen.
“Da dare ɗan wannan matan ya mutu domin ta kwanta a kansa.
20 Och hon stod upp om nattena, och tog min son ifrå mine sido, vid din tjenarinna sof, och lade honom på sin arm; och sin döda son lade hon på min arm.
Saboda haka ta tashi da tsakar dare ta ɗauki ɗana daga gefena yayinda baiwarka take barci. Sai ta sa shi kusa da ƙirjinta, ta kuma sa mataccen ɗanta kusa da ƙirjina.
21 Och då jag om morgonen uppstod, till att gifva min son dia, si, då var han död; men om morgonen såg jag granneliga på honom, och si, det var icke min son, den jag födt hade.
Kashegari, da na farka don in shayar da ɗana, sai na tarar ya mutu! Amma sa’ad da na dube shi da kyau da safe, sai na ga ashe ba ɗan da na haifa ba ne.”
22 Den andra qvinnan sade: Det är icke så; min son lefver, och din son är död. Men denna sade: Det är icke så; din son är död, och min son lefver; och talade alltså för Konungenom.
Amma ɗaya matar ta ce, “A’a! Mai rai ɗin ne ɗana; mataccen naki ne.” Amma ta farin ta nace, “A’a! Mataccen ne naki; mai ran ne nawa.” A haka suka yi ta gardama a gaban sarki.
23 Och Konungen sade: Denna säger: Min son lefver, och din son är död; den andra säger: Icke så; din son är död, och min son lefver.
Sarki ya ce, “Wannan ta ce, ‘Ɗana ne a raye, naki ne matacce,’ yayinda ɗayan tana cewa, ‘A’a! Ɗanki ne mataccen, nawa ne a raye.’”
24 Och Konungen sade: Tager mig hit ett svärd. Och då svärdet var buret fram till Konungen,
Sai sarki ya ce, “Kawo mini takobi.” Sai aka kawo takobi wa sarki.
25 Sade Konungen: Hugger det lefvande barnet i tu stycker, och gifver desso hälftena; och den andro ock hälftena.
Ya ba da umarni ya ce, “Yanka yaron nan mai rai, gida biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26 Då sade qvinnan, hvilkens barn lefde, till Konungen (ty hennes moderliga hjerta gaf sig öfver sin son): Ack! min Herre, gifver henne barnet lefvandes, och dräper det icke. Men den andra sade: Det vare hvarken mitt eller ditt, låt skiftat.
Ainihin mamar ɗan da yake a raye ta cika da tausayi saboda ɗanta, sai ta ce wa sarki, “Ina roƙonka, ranka yă daɗe, kada ka kashe yaron! Ka ba ta kawai!” Amma ɗayan matar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu ɗan da rai, a ci gaba a raba shi!”
27 Då svarade Konungen, och sade: Gifver desso barnet lefvandes, och dräper det icke; hon är dess moder.
Sai sarki ya zartar da hukuncinsa ya ce, “A ba da jariri mai ran ga mata ta fari. Kada a kashe shi; ita ce ainihin mahaifiyarsa.”
28 Och den domen, som Konungen afsagt hade, spordes för hela Israel, och de fruktade Konungen; förty de sågo, att Guds vishet var i honom till att döma.
Sa’ad da dukan Isra’ila suka ji hukuncin da sarki ya zartar, suka girmama sarki sosai, domin sun gane cewa Allah ya ba shi hikimar yin shari’ar adalci.

< 1 Kungaboken 3 >