< 1 Krönikeboken 21 >
1 Och Satan hof sig upp emot Israel, och gaf David in, att han lät räkna Israel.
Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
2 Och David sade till Joab, och till folkens öfverstar: Går bort, och räkner Israel, allt ifrå BerSeba intill Dan; och bärer till mig, att jag må veta talet.
Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
3 Joab sade: Herren föröke till sitt folk hundrade sinom så mycket som det nu är: Min herre Konung, äro de icke alle mins herras tjenare? Hvi frågar då min herre derefter? Hvi skulle en skuld komma på Israel?
Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
4 Men Konungens ord gick fram emot Joab; och Joab drog ut, och for omkring all Israel, och kom till Jerusalem;
Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
5 Och fick David talet på det räknade folket; och det var af hela Israel ellofva sinom hundrade tusend män, som svärd utdrogo; och Juda fyrahundrade sinom tusend, och sjutiotusend män, som svärd utdrogo.
Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
6 Men Levi och BenJamin räknade han intet ibland dessa; förty Konungens ord var Joab en styggelse.
Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
7 Men Gudi misshagade detta; och han slog Israel.
Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
8 Och David sade till Gud: Jag hafver svårliga syndat, att jag detta gjort hafver; men nu tag dins tjenares missgerning bort; förty jag hafver fast dårliga gjort.
Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
9 Och Herren talade med Gad, Davids Siare, och sade:
Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
10 Gack, tala med David, och säg: Detta säger Herren: Treggehanda sätter jag dig före; utvälj dig der ett af, det jag dig göra skall.
“Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
11 Då Gad kom till David, sade han till honom: Detta säger Herren:
Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
12 Utvälj dig, antingen tre hård år, eller tre månaders flykt för dina ovänner, och för dina fiendars svärd, det du icke undkomma kan; eller tre dagar Herrans svärd och pestilentie i landena, så att Herrans Ängel förderfvar i alla Israels gränsor; så se nu till, hvad jag skall svara honom, som mig utsändt hafver.
shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
13 David sade till Gad: Mig är fast ångest; dock vill jag falla i Herrans hand; ty hans barmhertighet är ganska stor; och icke falla i menniskohand.
Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
14 Då lät Herren komma pestilentie i Israel, så att sjutiotusend män föllo af Israel.
Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
15 Och Gud sände Ängelen till Jerusalem till att slå det; och när han förderfvade, såg Herren dertill, och ångrade det onda, och sade till Ängelen, som förderfvade: Det är nog, håll dina hand tillbaka. Men Herrans Ängel stod vid Arnans, den Jebuseens lado.
Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
16 Och David hof upp sin ögon, och fick se Herrans Ängel stå emellan himmelen och jordena, och ett draget svärd i hans hand, uträckt öfver Jerusalem. Då föll David och de äldste på sin ansigte, klädde i säcker.
Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
17 Och David sade till Gud: Är icke jag den som lät räkna folket? Jag är den som syndade och det onda gjort hafver; dessa far, hvad hafva de gjort? Herre, min Gud, låt dina hand vara emot mig och mins faders hus, och icke emot ditt folk, till plågo.
Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
18 Och Herrans Ängel sade till Gad, att han skulle säga David, att David skulle gå upp, och resa Herranom ett altare i Arnans, den Jebuseens, lado.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
19 Alltså gick David upp efter Gads ord, som han i Herrans Namn talat hade.
Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
20 Men då Arnan vände sig, och såg Ängelen, han och hans fyra söner med honom, gömde de sig bort; ty Arnan tröskade vete.
Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
21 Som nu David gick till Arnan, såg Arnan och vardt varse David, och gick utaf ladone, och tillbad David på sitt ansigte till jordena.
Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
22 Och David sade till Arnan: Gif mig ladones rum, att jag må bygga Herranom ett altare deruppå; för fulla penningar skall du få mig det, att plågan på folket må återvända.
Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
23 Arnan sade till David: Tag dig det, och gör, min herre Konung, såsom dig täckes. Si, jag gifver också oxarna till bränneoffret, och redskapen till ved, och hvete till spisoffer; alltsamman gifver jag det.
Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
24 Men Konung David sade till Arnan: Icke så, utan för fulla penningar vill jag köpat; ty jag vill icke taga det ditt är för Herranom, och göra bränneoffer till gifvins.
Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
25 Alltså gaf David Arnan, för rummet, gyldene siktar till vigt sexhundrad.
Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
26 Och David byggde dersammastäds Herranom ett altare, och offrade bränneoffer och tackoffer; och då han åkallade Herran, hörde han honom genom eld af himmelen uppå bränneoffrets altare.
Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
27 Och Herren sade till Ängelen, att han skulle sticka sitt svärd i skidona.
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
28 På samma tiden, då David såg, att Herren hade hört honom uppå Arnans den Jebuseens plats, offrade han der.
A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
29 Ty Herrans tabernakel, som Mose i öknene gjort hade, och bränneoffrets altare, var i den tiden på höjdene i Gibeon.
Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
30 Men David kunde icke gå ditin för det, till att söka Gud; så var han förskräckt för Herrans Ängels svärd.
Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.