< 1 Krönikeboken 20 >
1 Och då året omgånget var, på den tid som Konungar utdraga, utförde Joab hären, och förderfvade Ammons barnas land; kom och belade Rabba; men David blef i Jerusalem. Och Joab slog Rabba, och bröt det neder.
Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
2 Och David tog deras Konungs krono af hans hufvud, och fann deruti en centener gulds vigt och ädla stenar; och hon vardt satt på Davids hufvud; förde han ock ganska mycket rof utu staden.
Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
3 Men folket derinne förde han ut, och lät sönderdela dem med sågar och jernhackor och kilar; alltså gjorde David alla Ammons barnas städer. Och David drog med folkena till Jerusalem igen.
ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
4 Derefter hof sig en strid upp i Gaser med de Philisteer. På den tiden slog Sibbechai, den Husathiten, Sippai, den utaf Rephaims barnom var, och undertryckte honom.
Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
5 Och det hof sig ännu en strid upp med de Philisteer. Då slog Elhanan, Jairs son, Lahmi, Goliaths broder den Gitthiten, hvilkens spjutskaft var såsom ett väfträ.
Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
6 Åter vardt en strid i Gath. Der var en stor man, han hade sex finger och sex tår, det gör fyra och tjugu. Han var också födder af Rapha.
Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
7 Han bespottade Israel; men Jonathan, Simea son, Davids broders, slog honom.
Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
8 Desse voro födde af Rapha i Gath, och föllo genom Davids och hans tjenares hand.
Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.