< Zaburi 80 >

1 Usikie, Mchungaji wa Israel, wewe uliye muongoza Yusufu kama kundi; wewe uketiye juu ya makerubi, utuangazie!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 Machoni pa Efraimu na Benjamini na Manase, uziinue nguvu zako; njoo na utuokoe.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Mungu, uturejeshe sisi; uangaze uso wako juu yetu, nasi tutaokolewa.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 Yahwe Mungu wa majeshi, mpaka lini utawakasirikia watu wako wanapoomba?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 Umewalisha wa mkate wa machozi na umewapa machozi ili wanywe katika kiasi kikubwa.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 Umetufanya kitu kwa ajili ya majirani zetu kubishania, na maadui zetu hucheka kuhusu sisi kati yao.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 Mungu wa majeshi, uturejeshe sisi; nasi tutaokolewa.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 Wewe ulileta mzabibu kutoka Misri; ukawafukuza mataifa na ukaupanda.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 Uliisafisha ardhi kwa ajil yake; nao ulipata mzizi na kuijaza nchi.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 Milima ilifunikwa kwa kivuli chake, mierezi ya Mungu kwa matawi yake.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 Ilieneza matawi yake mbali kama bahari na mashina yake mpaka kwenye Mto Euphrates.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 Kwa nini umezibomoa kuta zake hata wapitao karibu huyachuma matunda yake.
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 Ngurue wa msituni wanauharibu, na wanyama wa kondeni wanaula.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Urudi, Ee Mungu wa majeshi; kutoka mbinguni utazame chini na uuangalie na kuujali huu mzabibu.
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 Huu ni mzizi ambao mkono wako wa kuume umeupanda, mashina ambayo wewe uliyafanya yakue.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 Yamekatwa na kuchomwa; yameangamia kwa sababu ya kukemea kwako.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Mkono wako na uwe juu ya mtu aliye mkono wako wa kuume, kwa mwana wa mtu uliyemfanya imara kwa ajili yako mwenyewe.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 Ndipo hatuta kuacha wewe; utuhuishe, nasi tutaliita jina lako.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 Yahwe, Mungu wa majeshi, uturejeshe sisi; utuangazie nuru ya uso wako, nasi tutaokolewa.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Zaburi 80 >