< Zaburi 47 >
1 Pigeni makofi, enyi watu wote; mpigieni Mungu kelele za ushindi.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Kwa maana Yahwe Aliye Juu anatisha; ni Mfalme mkuu dunia yote.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Yeye anawatiisha chini yetu na mataifa chini ya miguu yetu.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Yeye huchagua urithi kwa ajili yetu, utukufu wa Yakobo ambaye alimpenda. Serah
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Mungu ameinuliwa juu kwa shangwe, Kwa mbiu ya shangwe Yahwe yu juu.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Mwimbieni Mungu sifa, imbeni sifa; mwimbieni sifa Mfalme wetu, imbeni sifa.
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Kwa maana Mungu ni Mfalme duniani kote; mwimbieni mkiwa na uelewa.
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Mungu anatawala mataifa yote; Mungu hukaa kwenye kiti cha enzi.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Wakuu wa watu wamekusanyika pamoja kwa watu wa Mungu wa Ibrahimu; kwa kuwa ngao za duniani ni za Mungu; yeye ameinuliwa juu sana.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.