< Zaburi 44 >

1 Mungu, tumesikia kwa masikio yetu, baba zetu wametuambia kazi uliyofanya katika siku zao, siku za kale.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Uliwafukuza mataifa kwa mkono wako, lakini ukawafanya watu wetu kuishi humo; wewe uliwataabisha mataifa, lakini ukawaeneza watu wetu katika nchi.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Kwa maana hawakupata umiliki wa nchi kwa upanga wao, wala mkono wao wenyewe haukuwaokoa; bali mkono wako wakuume, mkono wako, na nuru ya uso wako, na kwa sababu uliwaridhia.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Mungu, wewe ni Mfalme wangu, amuru ushindi kwa ajili ya Yakobo.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Kwa uweza wako tutawaangusha chini maadui zetu; kwa jina lako tutatembea juu yao, wale wanao inuka dhidi yetu.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Kwa maana sitauamini upinde wangu, wala upanga wangu hautaniokoa.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Bali wewe ndeye uliyetuokoa na adui zetu, na umewaaibisha wale watuchukiao.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Katika Mungu tumefanywa kujivuna siku zote, nasi tutalishukuru jina lako milele. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Lakini sasa umetutupa na kutufedhehesha, na hauendi na majeshi yetu.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Umetufanya kuwakimbia maadui zetu; na wale watuchukiao huchukua vitu vyetu vya thamani kwa ajili yao wenyewe.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Umetufanya kama kondoo aliyeandaliwa kwa ajili ya chakula na umetutawanya kati ya mataifa.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Wewe unawauza watu wako bure; kwa kufanya hivyo haukupata faida.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Wewe umetufanya kukemewa na majirani zetu, kuchekwa, na kudhihakiwa na wale wanao tuzunguka.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Umetufaya kituko kati ya mataifa, .......................................................
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Siku zote fedheha yangu iko mbele yangu, na aibu ya uso wangu imenifunika
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 kwa sababu ya sauti yake iliyo kemea na kutukana, kwa sababu ya adui na kisasi.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Yote haya yametupata sisi; bado hatukukusahau wewe wala kulikosea agano lako.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Mioyo yetu haikukengeuka; hatua zetu hazikuiacha njia yako.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Bali wewe umetuadhibu vikali katika mahali pa mbweha na kutufunika na uvuli wa mauti.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Ikiwa tumelisahau jina la Mungu wetu au kueneza mikono yetu kwa Mungu mgeni,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Mungu asingeligundua hili? Kwa maana yeye anazijua siri za moyo.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Hakika, kwa ajili ya jina lako tutauawa siku zote; tunahesabiwa kuwa kondoo kwa ajili ya kuchinjwa.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Bwana, amka, kwa nini unalala? Inuka, usitutupe moja kwa moja.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Kwa nini unaficha uso wako na kusahau mateso yetu na kukandamizwa kwetu?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Kwa maana tumeyeyushwa kwenye mavumbi; miili yetu imeshikamana na ardhi.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Inuka utusaidie na utuokoe kwa ajili ya uaminifu wa agano lako.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Zaburi 44 >