< Zaburi 107 >

1 Mshukuruni Yahwe, maana ni mwema, na uaminifu wa agano lake wadumu milele.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Waseme hivi waliokombolewa na Yahwe, wale aliowaokoa toka mkononi mwa adui.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Yeye amewakusanya kutoka nchi za kigeni, kutoka mashariki na magharibi, kutoka kaskazini na kusini.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Walitanga-tanga janwani katika njia ya nyika hawakuona mji wa kuishi.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Kwa sababu walikuwa na njaa na kiu, walikata tamaa kutokana na uchovu.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Kisha walimuita Yahwe katika shida yao, naye aliwaokoa toka katika dhiki yao.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Aliwaongoza kupitia njia ya moja kwa moja waweze kwenda mjini kuishi humo.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Oh ili watu wamsifu Yahwe kwa ajili ya uaminifu wa agano lake na kwa mambo ya ajabu aliowatendea wanadamu!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Maana hutosheleza shauku za walio na kiu, na hamu ya wale wenye njaa yeye huwashibisha kwa mambo mema.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Baadhi walikaa katika giza na uvuli wa mauti, walifungwa katika mateso na minyororo.
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Hii ni kwa sababu walikuwa wameliasi neno la Mungu na walikataa maelekezo ya Aliye Juu.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Aliinyenyekesha mioyo yao kupitia magumu; walipata mashaka na hakukuwa na mmoja wa kuwasaidia.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Kisha wakamwita Yahwe katika shida yao, naye akawatoa katika dhiki yao.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Aliwatoa gizani na kwenye uvuli wa mauti na kuvunja vifungo vyao.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Oh ili watu wamsifu Yahwe kwa ajili ya uaminifu wa agano lake na kwa mambo ya ajabu aliyoyatenda kwa wanadamu!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Kwa maana amevunja malango ya shaba na kukata mapingo ya chuma.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Walikuwa wapumbavu katika njia zao za uasi na kuteswa kwa sababu ya dhambi zao.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Walipoteza hamu yao ya kula chakula chochote, na waliyakaribia malango ya kifo.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Kisha walimlilia Yahwe katika shida yao, naye akawatoa katika dhiki yao.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Alituma neno lake na likawaponya, na akawaokoa kutoka katika uharibifu wao.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Oh ili watu wamsifu Yahwe kwa ajili ya uaminifu wa agano lake na kwa mambo ya ajabu aliyoyatenda kwa wanadamu!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Na watoe dhabihu ya shukrani na kutangaza matendo yake kwa kuimba.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Baadhi husafiri baharini katika meli na kufanya biashara juu ya bahari.
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Hawa huona matendo ya Yahwe na maajabu yake baharini.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Kwa maana aliamuru na alivumisha upepo wa dhoruba ambao uliyainua juu mawimbi ya baharini.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Walipanda juu mawinguni na kushuka vilindini. Nafsi zao ziliyeyuka katika dhiki.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Waliyumba-yumba na kupepesuka kama walevi na hawakujua la kufanya.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Kisha walimlilia Yahwe katika shida yao, naye akawatoa katika dhiki yao.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Aliituliza dhoruba, na mawimbi yakatulia.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Ndipo walifurahia kwa sababu bahari ilikuwa shwali, na aliwaleta kwenye bandari waliyoitamani.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Oh, ili watu wamsifu Yahwe kwa ajili ya uaminifu wa agano lake na kwa mambo ya ajabu aliyowatendea wanadamu!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Wamtukuze yeye katika kusanyiko la watu na wamsifu yeye katika baraza la viongozi.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Aligeuza mito ikwa jangwa, chemchem ya maji ikawa nchi kame,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 na nchi ya matunda mengi ikawa nchi isiyozaa kwa sababu ya uovu wa watu wake.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Aligeuza jangwa likawa ziwa la maji na nchi kame ikawa chemchem ya maji.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Aliwakalisha huko wenye njaa, nao walijenga mji na kuishi humo.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Walijenga mji ili kupanda mimea shambani, kupanda mizabibu, na kuleta humo mazao tele.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Yeye huwabariki wameongezeka sana katika hesabu. Haachi mifugo yao ipungue katika hesabu.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Kisha wakapungua na kudhilika kwa dhiki na mateso.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Akawamwagia viongozi dharau na akawafanya wazunguke katika jangwa, mahali pasipo na njia.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Lakini aliwalinda wahitaji dhidi ya mateso na kujali kwa ajili ya familia yake kama kundi la kondoo.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Wenye haki wataona hili na kufurahi, na uovu wote utaona na kufunga kinya chake.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Yeyote mwenye hekima anapaswa kuyaangalia haya na kutafakari juu ya matendo ya uaminifu wa agano la Yahwe.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Zaburi 107 >