< Zaburi 104 >
1 Nitamsifu Yahwe maisha yangu yote, Ewe Yahwe Mungu wangu, wewe ni mkubwa sana; umevikwa kwa utukufu na enzi.
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 Unajifunika mwenyewe kwa nuru kama kwa mavazi; umetandaza mbingu kama pazia za hema.
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 Umeweka mawinguni mihimili ya vyumba vyako; huyafanya mawingu gari lako; hutembea juu ya mbawa za upepo.
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 Yeye huufanya upepo kuwa wajumbe wake, miale ya moto kuwa watumishi wake.
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 Aliiweka misingi ya nchi, nayo haitahamishwa kamwe.
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 Wewe uliifunika nchi kwa maji kama kwa mavazi; maji yalifunika milima.
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 Kukemea kwako kulifanya maji kupungua; kwa sauti ya radi yako yakaondoka kasi.
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 Milima iliinuka, na mabonde yakaenea mahali ambapo wewe ulikwisha pachagua kwa ajili yao.
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 Umeweka mipaka kwa ajili yao ambao hayawezi kuupita; hayawezi kuifunika nchi tena.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 Yeye alifanya chemchemi kutiririsha maji mabondeni; mito kutiririka katikati ya milima.
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 Inasambaza maji kwa ajili ya wanyama wote wa shambani; punda wa porini hukata kiu yao.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 Kandokando ya mito ndege hujenga viota vyao; huimba kati ya matawi.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 Humwagilia milima kutoka katika chumba chake cha maji mawinguni. Nchi imejazwa kwa matunda ya kazi yake.
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 Huzifanya nyasi kukua kwa ajili ya mifugo na mimea kwa ajili ya binadamu kulima ili kwamba mwanadamu aweze kuzalisha chakula toka nchini.
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 Hutengeneza mvinyo kumfurahisha mwanadamu, mafuta yakumfanya uso wake ung'ae, na chakula kwa ajili ya kuimarisha uhai wake.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 Miti ya Yahwe hupata mvua nyingi; Mierezi ya Lebanoni aliyoipanda.
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 Hapo ndege hutengeneza viota vyao. Na korongo, misunobari ni nyuma yake.
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 Mbuzi mwitu huishi kwenye milima mrefu; na urefu wa milima ni kimilio la wibari.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 Aliuchagua mwezi kuweka alama ya majira; jua latambua kuchwa kwake.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 Wewe hufanya giza la usiku ambapo wanyama wote wa msituni hutoka nje.
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 Wana simba huunguruma kwa ajili ya mawindo na hutafuta chakula chao kutoka kwa Mungu.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 Jua linapochomoza, huenda zao na kujilaza mapangoni mwao.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 Wakati huo huo, watu hutoka nje kuelekea kazi zao na utumishi wake mpaka jioni.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 Yahwe, ni jinsi gani kazi zako zilivyo nyingi na za aina mbalimbali! Kwa hekima ulizifanya zote; nchi inafurika kwa kazi zako.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 Kule kuna bahari, yenye kina kirefu na pana, ikiwa na viume vingi visivyo hesabika, vyote vidogo na vikubwa.
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 Meli husafili humo, na ndimo alimo Lewiathani uliye muumba acheze baharini.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 Hawa wote hukutazama wewe uwape chakula kwa wakati.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 Unapowapa chakula, hukusanyika; ufunguapo mkono wako, wanatosheka.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 Unapouficha uso wako, wanateseka; ukiiondoa pumzi yao, wanakufa na kurudi mavumbini.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 Unapotuma Roho yako, wanaumbwa, nawe unaifanya upya nchi.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 Utukufu wa Yahwe na udumu milele; Yahwe na aufurahie uumbaji wake.
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 Yeye hutazama nchi, nayo hutikisika; huigusa milima, nayo hutoa moshi.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 Nitamwimbia Yahwe maisha yangu yote; nitamwimbia sifa Mungu wangu nigali ninaishi.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 Mawazo yangu na yawe matamu kwake; nitafurahia katika Yahwe.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Wenye dhambi na waondoshwe katika nchi, na waovu wasiwepo tena. Ninamsifu Yahwe maisha yangu yote. Msifuni Yahwe.
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.