< Mithali 22 >
1 Jina jema huchaguliwa dhidi ya utajiri mwingi na fadhila ni bora kuliko fedha na dhahabu.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 Watu matajiri na masikini wanafanana katika hili - Yehova ni muumba wao wote.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 Mtu mwenye hekima huiona taabu na kujificha mwenyewe, bali mjinga huendelea mbele na huumia kwa ajili yake.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 Thawabu ya unyenyekevu na kumcha Yehova ni utajiri, heshima na uzima.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Miiba na mitego hulala katika njia ya wakaidi; yeye anayelinda maisha yake atakuwa mbali navyo.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Mfundishe mtoto njia inayompasa na wakati akiwa mzee hatayaacha mafundisho hayo.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 Watu matajiri huwatawala watu masikini na mwenye kukopa ni mtumwa wa yule anayekopesha.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 Yule anayepanda udhalimu atavuna taabu na fimbo ya hasira yake itanyauka.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 Mwenye jicho la ukarimu atabarikiwa, maana anashiriki mkate wake pamoja na masikini.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Mfukuze mbali mwenye dhihaka, na ugomvi utaondoka, mashindano na matukano yatakoma.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 Anayependa moyo safi na mwenye maneno ya neema, atakuwa rafiki yake mfalme.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 Macho ya Yehova huyaangalia maarifa, bali huyapindua maneno ya wadanganyifu.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 Mtu mvivu husema, “Kuna simba mtaani! Nitauwawa sehemu za njia.”
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 Kinywa cha malaya ni shimo lenye kina kirefu; hasira ya Yehova huchochewa dhidi ya yule anayetumbukia ndani yake.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 Upumbavu umefungwa katika moyo wa mtoto, lakini marudi ya fimbo huutoa.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 Anayewanyanyasa watu masikini ili kuongeza mali yake, au kuwapa matajiri, atakuwa masikini.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Tega sikio lako na usikilize maneno ya wenye busara na utumia moyo wako katika maarifa yangu,
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 maana itakuwa furaha kwako kama utayaweka ndani yako, kama yote yatakuwa katika midomo yako.
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 Basi tumaini lako liwe kwa Yehova, ninayafundisha kwako leo- hata kwako.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 Sijakuandikia wewe misemo thelathini ya mafundisho na maarifa,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 kwa kukufundisha kweli katika maneno haya yenye uaminifu, ili uwe na majibu yenye kutegemewa kwa waliokutuma?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 Usimwibie masikini kwa sababu ni masikini, au kumponda kwenye lango,
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 maana Yehova ataitetea kesi yao, na atawaibia uzima wale waliowaibia masikini.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 Usifanye urafiki na mtu mwenye kutawaliwa na hasira na wala usiambatane pamoja na mwenye hasira kali,
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 au utajifunza njia zake na utakuwa chambo kwa nafsi yako.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 Usiwe miongoni mwao wapigao mikono, mwenye kuahidi madeni.
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 Kama umekosa njia za kulipa, nini kitaweza kuzuia mtu kuchukua kitanda chako chini yako?
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 Usiondoe jiwe la mpaka la wahenga ambalo baba zako wameweka.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 Je umemwona mtu aliyeuwawa kwenye kazi yake? Atasimama mbele ya wafalme; hatasimama mbele ya watu wa kawaida.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.