< Mithali 21 >

1 Moyo wa mfalme ni mfereji wa maji katika mkono wa Yehova; anaugeuza popote anakopenda.
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
2 Kila njia ya mtu ni sawa katika macho yake mwenyewe, lakini ni Yehova anayeipima mioyo.
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
3 Kutenda haki na adili hukubaliwa zaidi na Yehova kuliko sadaka.
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
4 Macho ya kiburi na moyo wa majivuno- taa ya waovu- ni dhambi.
Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
5 Mipango ya mwenye juhudi huelekea kwenye mafanikio tu, bali kila mtu anayetenda kwa haraka huelekea umasikini.
Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
6 Kujipatia utajiri kwa ulimi wa uongo ni mvuke unaopita upesi na mtego ambao unafisha.
Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
7 Vurugu ya waovu itawaburuta mbali, maana wanakataa kutenda haki.
Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
8 Njia ya mwenye hatia ni ukatiri, bali mwenye usafi hutenda yaliyo ya haki.
Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
9 Bora kuishi kwenye kona ya juu darini kuliko katika nyumba pamoja na mke mgonvi.
Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
10 Hamu ya mwovu ni uchu wa mabaya; jirani yake haoni ukarimu katika macho yake.
Mugun mutum yakan zaƙu ya aikata mugunta; maƙwabcinsa ba ya samun jinƙai daga gare shi.
11 Mwenye dhihaka anapoadhibiwa mjinga hupata busara, na mtu mwenye busara anapofundishwa, anaongeza maarifa.
Sa’ad da aka hukunta mai ba’a marasa azanci suka yi wayo; sa’ad da aka yi wa mai hikima umarni yakan sami sani.
12 Atendaye haki huilinda nyumba ya mwovu; huwashusha waovu kwenye uharibifu.
Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
13 Anayeziba masikio yake kwenye kilio cha masikini, pia atalia, lakini hatajibiwa.
In mutum ya toshe kunnuwansa ga kukan matalauci, shi ma zai yi kukan neman taimako ba kuwa zai sami amsa ba.
14 Zawadi ya siri hutuliza hasira na zawadi ya kificho hutuliza ghadhabu kuu.
Kyautar da aka yi a asirce takan kwantar da fushi, kuma cin hancin da aka rufe a cikin riga kan tā da fushi mai tsanani.
15 Haki ikitendeka, huleta furaha kwa mwenye kutenda wema, lakini huleta hofu kubwa kwa watenda mabaya.
Sa’ad da aka yi adalci, yakan kawo farin ciki ga mai adalci amma fargaba ga masu aikata mugunta.
16 Yule anayezurura kutoka kwenye njia ya ufahamu, atapumzika kwenye kusanyiko la wafu.
Mutumin da ya kauce daga hanyar fahimi kan zo ga hutu a ƙungiyar matattu.
17 Anayependa raha atakuwa masikini; anayependa divai na mafuta hawezi kuwa tajiri.
Duk mai son jin daɗi zai zama matalauci; duk mai son ruwan inabi da mai ba zai taɓa zama mai arziki ba.
18 Mtu mbaya ni fidia kwa yule atendaye haki, na mdanganyifu ni fidia kwa waaminifu.
Mugu kan zama abin fansa don adali, marar aminci kuma don mai aikata gaskiya.
19 Bora kuishi jangwani kuliko kuishi pamoja na mwanamke ambaye huchochea sana ugomvi na malalamiko.
Gara a zauna a hamada da a zauna da mace mai fitina da kuma mugun hali.
20 Hazina yenye thamani na mafuta vipo nyumbani kwa mwenye busara, bali mtu mpumbavu huviharibu.
A gidan mai hikima akwai wuraren ajiya na abinci da mai masu kyau, amma wawa kan cinye duk abin da yake da shi.
21 Mtu atendaye haki na mwema -huyu mtu hupata uzima, haki na heshima.
Duk wanda ya nemi adalci da ƙauna kan sami rai, wadata da girmamawa.
22 Mtu mwenye busara huupima mji wa mashujaa, na huiangusha ngome wanayoitumaini.
Mutum mai hikima kan fāɗa wa birnin jarumawa ya kuma rushe katangar da suka dogara a kai.
23 Anayelinda kinywa chake na ulimi wake hujilinda mwenyewe na taabu.
Duk wanda yake lura da bakinsa da kuma harshensa kan kiyaye kansa daga masifa.
24 Mtu mwenye kiburi na maringo- “Dhihaka” ndilo jina lake - hutenda kwa majivuno na kujidai.
Mai girmankai da kuma mai fariya, “Mai ba’a” ne sunansa; yana yin abubuwa da girmankai ainun.
25 Shauku ya mtu mvivu itamuua, maana mikono yake hukataa kufanya kazi.
Marmarin rago zai zama mutuwarsa, domin hannuwansa sun ƙi su yi aiki.
26 Kwa siku nzima hupatwa na uchu na uchu zaidi, lakini atendaye haki hutoa na wala hazuii.
Dukan yini yana marmari ya sami ƙari, amma mai adalci yakan bayar hannu sake.
27 Sadaka ya mwovu ni chukizo; huwa ni chukizo zaidi anapoileta kwa nia mbaya.
Hadayar mugaye abin ƙyama ne, balle ma in aka kawo da mugun nufi!
28 Shahidi wa uongo ataangamia, bali anayesikiliza ataongea kwa muda wote.
Mai ba da shaidar ƙarya zai hallaka, kuma duk wanda ya saurare shi zai hallaka har abada.
29 Mtu mwovu huufanya uso wake kuwa mgumu, bali mtu mwadilifu ni thabiti juu ya njia zake.
Mugun mutum kan yi tsayin daka, amma mai aikata gaskiya kan yi tunani a kan abin da yake yi.
30 Hakuna hekima, hakuna ufahamu, na hakuna shauri linaloweza kusimama kinyume na Yehova.
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
31 Farasi hutayarishwa kwa siku ya mapigano, lakini ushindi hupatikana kwa Yehova.
Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.

< Mithali 21 >