< Mithali 18 >

1 Yule ambaye hujitenga hutafuta matakwa yake mwenyewe na hupingana na hukumu zote za kweli.
Mutumin da ba ya abokantaka yakan nema ya cika burinsa ne kaɗai; yakan ƙi yarda da kowace maganar da take daidai.
2 Mpumbavu hapati raha katika ufahamu, lakini hufunua kile kilichopo katika moyo wake.
Wawa ba ya sha’awa ya sami fahimta amma abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya ba da ra’ayinsa.
3 Mtu mwovu anapokuja, dharau huja pamoja naye- sambamba na aibu na shutuma.
Sa’ad da mugunci ya zo, reni ma kan zo, haka kuma sa’ad da kunya ta zo, shan kunya kan biyo.
4 Maneno ya kinywa cha mtu ni maji yenye kina kirefu; chemchemi ya hekima ni mkondo unaotiririka.
Kalmomin bakin mutum suna da zurfi kamar ruwaye, amma maɓulɓulan hikima rafi ne mai gudu.
5 Si vema kuwa na upendeleo kwa mwovu, wala haifai kukana haki kwa wale watendao mema.
Ba shi da kyau ka yi wa mugu alheri ko ka hana wa marar laifi adalci.
6 Midomo ya mpumbavu huletea mafarakano na kinywa chake hukaribisha mapigo.
Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
7 Kinywa cha mpumbavu ni uharibifu wake na hujinasa mwenye kwa midomo yake.
Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
8 Maneno ya mmbea ni kama chembe tamu na hushuka katika sehema za ndani sana kwenye mwili.
Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
9 Basi, ambaye ni mzembe katika kazi yake ni ndugu yake anayeharibu wengi.
Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
10 Jina la Yehova ni mnara imara; atendaye haki hukimbilia na kuwa salama.
Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
11 Mali ya tajiri ni mji wake imara na katika fikira zake ni kama ukuta mrefu.
Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
12 Moyo wa mtu huwa na kiburi kabla ya anguko lake, bali unyenyekevu hutangulia kabla ya heshima.
Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
13 Anayejibu kabla ya kusikiliza- ni upuuzi na aibu yake.
Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
14 Roho ya mtu itajinusuru na madhara, bali roho iliyopondeka nani anaweza kuivumilia?
Sa rai da mutum ke yi kan taimake shi sa’ad da yake ciwo, amma in ya karai, to, tasa ta ƙare.
15 Moyo wa mwenye akili hujipatia maarifa na usikivu wa mwenye busara huitafuta.
Zuciya mai la’akari kan nemi sani; kunnuwan mai hikima kan bincika don yă koya.
16 Zawadi ya mtu inaweza kufungua njia na kumleta mbele ya mtu muhimu.
Kyauta kan buɗe hanya wa mai bayarwa yakan kuma kai shi a gaban babban mutum.
17 Wa kwanza kujitetea katika shitaka lake huonekana kuwa na haki hadi mpinzani wake aje na kumuuliza maswali.
Wanda ya fara mai da jawabi yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai wani ya fito ya yi masa tambaya tukuna.
18 Kupiga kura kunamaliza mabishano na kuwatawanya wapinzani imara.
Jefa ƙuri’a kan daidaita tsakanin masu faɗa ta kuma ajiye masu faɗan a rabe.
19 Ndugu aliyechukizwa ni mgumu kushawishiwa kuliko mji wenye nguvu, na kugombana ni kama makomeo ya ngome.
Ɗan’uwan da aka yi wa laifi ya fi birni mai katanga wuyan shiryawa, kuma faɗace-faɗace suna kama da ƙofofin ƙarfe na fada.
20 Tumbo la mtu litashiba kutoka kwenye tunda la kinywa chake; atatoshelezwa kwa mavuno ya midomo yake.
Daga abin da baki ya furta ne cikin mutum kan cika; girbi daga leɓunansa kuma yakan ƙoshi.
21 Uzima na kifo hutawaliwa kwa ulimi, na wale wenye kuupenda ulimi watakula tunda lake.
Harshe yana da ikon rai da mutuwa, kuma waɗanda suke ƙaunarsa za su ci amfaninsa.
22 Yeye apataye mke anapata kitu chema na kupokea fadhila kutoka kwa Yehova.
Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
23 Mtu masikini huomba rehema, lakini mtu tajiri hujibu kwa ukali.
Matalauci kan yi roƙo da taushi, amma mawadaci kan amsa da kakkausar murya.
24 Anayejidai kwa marafiki wengi watamleta katika uharibifu, bali yupo rafiki ambaye huwa karibu kuliko ndugu.
Mutum mai abokai masu yawa kan lalace, amma akwai abokin da yakan manne kurkusa fiye da ɗan’uwa.

< Mithali 18 >