< Ayubu 33 >

1 Kwahiyo sasa, nakuomba wewe, Ayubu, usikilize hotuba yangu; sikiliza maneno yangu yote.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Tazama sasa, nimeufumbua mdomo wangu; ulimi wangu umesema maneno ndani ya mdomo wangu.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Maneno yangu yatasema uadilifu wa moyo wangu; yatasema kwa unyofu yale ambayo mdomo wangu unayajua.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 Roho ya Mungu imeniumba; pumzi ya Mwenye nguvu imenipatia uhai.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Kama unaweza, nijibu; weka maneno yako katika mpangilio mbele yangu na kisha usimame.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Tazama, niko kama wewe ulivyo mbele za Mungu; nimeumbwa pia kutoka katika udongo.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Ona, tishio langu halitakufanya wewe uogope; wala mzigo wangu hautakuwa mzito kwako.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Umesema kwa hakika katika masikio yangu; nimeisikia sauti ya maneno yakeo yakisema,
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 'Mimi ni safi na bila hila; sina hatia, na hakuna dhambi ndani yangu.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Tazama, Mungu huona nafasi za kunishambulia mimi; huniangalia mimi kama adui yake.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Huweka miguu yangu akiba; naye huangalia njia zangu zote.'
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Tazama, katika hili hauko sawa, nitakujibu, kwa kuwa Mungu ni mkuu kuliko mtu.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Kwanini unashindana naye? Huwa hahesabu matendo yake yoyote.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Kwa kuwa Mungu huzungumza mara moja, naam, mara mbili, ingawa mwanadamu hawezi kutambua.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Katika ndoto, katika maono ya usiku, wakati usingizi mzito unapowapata watu, katika usingizi kitandani -
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 basi Mungu hufungua masikio ya watu, na kuwatisha kwa vitisho,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 kwa kusudi la kumvuta mtu atoke katika makusudio yake maovu, na kuyaweka majivuno mbali naye.
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Mungu huyaokoa maisha ya mwanadamu kutoka katika shimo, na uhai wake dhidi ya kifo.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Mtu huadhidibiwa pia na maumivu kitandani mwake, na maumivu makali yanayodumu katika mifupa yake,
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 ili kwamba maisha yake yachukie chakula, na roho yake ichukie vyakula vizuri.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Nyama yake imeharibiwa ili kwamba usionekane; mifupa yake, mara moja isionekane, sasa basi ng'ang'ania.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Hakika, roho yake inasogea shimoni, na uhai wake unasogea kwa wale wanaotaka kuuharibu.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Lakini kama kuna malaika anayeweza kuwa mpatanishi kwa ajili yake, mpatanishi mmoja miongoni mwa maelfu ya malaika, kumwonesha kile kilicho cha haki ili atende haki,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 na kama malaika ni mpole kwake na kumwambia Mungu, 'Mwokoe mtu huyu ili asishuke chini shimoni; nimepata fidia kwa ajili yake,'
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 kisha mwili wake utakuwa mororo kuliko mwili wa mtoto, atazirudia siku za nguvu za ujana wake.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Atamwomba Mungu, na Mungu atakuwa mwema kwake, ili kwamba auone uso wa Mungu akiwa mwenye furaha. Mungu atampa mtu ushindi wake.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Ndipo mtu huyo ataimba mbele ya watu wengine na kusema, 'Nilitenda dhambi na kuasi kile kilichokuwa cha haki, lakini dhambi yangu haikuadhibiwa.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Mungu ameiokoa roho yangu isiende chini shimoni; maisha yangu yataendelea kuuona mwanga.'
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Tazama, Mungu hufanya mambo haya yote pamoja na mwanadamu, mara mbili, naam, hata mara tatu,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 kuirudisha roho yake kutoka shimoni, ili kwamba aweze kumlikwa na mwanga wa maisha.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Ayubu, zingatia na unisikilize mimi; nyamaza nami nitasema.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Ikiwa una kitu cha kusema, na unijibu; sema, maana nataka kuhakikisha kwamba wewe uko katika haki.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Kama sivyo, basi nisikilize, ubaki kimya, nami nitakufundisha wewe hekima.”
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Ayubu 33 >