< Ayubu 27 >

1 Ayubu akaendelea kuoengea na kusema,
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 “Kama aishivyo Mungu, ameniondolea haki yangu, Mwenyezi, aliyeyafanya machungu maisha yangu,
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 kadili uhai ungalimo ndani yangu uzima wa Mungu upo puani mwangu.
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Hakika midomo yangu haitanena uovu, wala ulimi wangu kunena uongo.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Sitakiri kwamba mko sahihi; hata nifapo sitakana uadilifu wangu.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Naishikilia haki yangu na sitaiacha; nafsi yangu haitanisuta kadili ninavyoishi.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 Adui yangu na awe kama mwovu; anayeinuka kunyume changu na awe kama asiye haki.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Kwani tumaini la mwovu ni nini Mungu anapomwondoa, Mungu anapochukua uhai wake?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Je Mungu atasikiliza kilio chake tabu zinapompat?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Je atajifurahisha katika Mwenyezi na kumwita Mungu nyakati zote
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Nitawafundisha kuhusu uwezo wa Mungu; sitabatilisha mawazo ya Mwenyezi.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Tazama, ninyi nyote mmeona; kwa nini basi mmeongea yasiyo na maana.
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Hii ndiyo hatima ya waovu mbele za Mungu, urithi wa mtesaji aupokeao kutoka kwa Mwenyezi.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Ikiwa watoto wake wataongezeka, ni kwa upanga; uzao wake utakuwa na njaa.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Wanaomsalia watauawa kwa tauni, na wajane wao hawatawaombolezea.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 Japokuwa waovu hurundika mali kama mavumbi,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 na kukusanya mavazi kama udongo, atakusanya mavazi, lakini mwenye haki atavaa, na wasio na hatia watagawana mali.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Hujenga nyumba yake kama buibui, kama kibanda cha muda afanyacho mlinzi.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Hulala kitandani akiwa tajiri, lakini hataendelea hivyo; na afumbuapo macho, hana kitu.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Vitisho humpata kama maji, dhoruba humwondoa usiku.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Upepo wa mashariki umwondoa, naye huondoka; humwondoa mahali pake.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Humpiga bila kukoma; hujaribu kumnasua katika uwezo wake.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Unampigia makofi kwa kejeli; humwondoa mahali pake.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Ayubu 27 >