< Ayubu 21 >

1 Kisha Ayubu akajibu na kusema,
Sai Ayuba ya amsa,
2 “Sikilizeni hotuba yangu kwa makini, hii na iwe faraja yenu.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Nimeteswa, lakini pia nitasema; nikisha kusema, endeleeni kudhihaki.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Lakini kwangu mimi, malalamikio yangu ni kwa mtu? Kwa nini nisiwe mwenye subira?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Nitazameni na mshangae, nanyi wekeni mkono wenu midomoni mwenu.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Ninapoyafikiria mateso yangu, ninaumizwa, mwili wangu unaogopa.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Kwa nini waovu wanaendelea kuishi, wanazeeka, na kuwa na uwezo katika madaraka?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Wazao wao wanathibitishwa mbele zao, na uzao wao unaimarika machoni pao.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Nyumba zao ziko salama mbali na hofu; wala fimbo ya Mungu haiko juu yao.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Dume lao la ng'ombe linazalisha; halishindwi kufanya hivyo; ng'ombe wao anazaa na hafishi ndama wake akiwa mchanga.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Wanawapeleka wadogo wao kama kundi la kondoo, na watoto wao hucheza.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Wanaimba kwa tari na vinubi na hufurahi kwa muziki na zomari.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Wanatumia siku zao katika mafanikio, na wanashuka kuzimu kwa utulivu. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Wanamwambia Mungu, 'Ondoka kwetu kwani hatutaki ufahamu wowote juu ya njia zako.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Mwenye enzi ni nani, hata tumwabudu? Tutafaidika na nini tukimwabudu? Tutapata faida gani ikiwa tutamwomba?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Tazama, je mafanikio yao hayamo katika mikono yao wenyewe? Sina cha kufanya na ushauri wa waovu.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Mara ngapi taa za waovu huzimwa, au kwamba majanga huja juu yao? Mara ngapi inatokea kwamba Mungu husambaza huzuni kwao kwa hasira?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Ni mara ngapi inatokea kwamba wanakuwa kama mabua mbele ya upepo au kama makapi yanayopeperushwa na dhoruba?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Mnasema, 'Mungu huweka hatia ya mtu kwa watoto wake kuilipa.' Na alipe yeye mwenyewe, ili kwamba aweze kujua hatia yake mwenyewe.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Acha macho yake yaone uangamivu wake mwenyewe, na acha anywe gadhabu ya Mwenyezi.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Kwani anaangaliaje familia yake mbele yake idadi ya miezi yake inapokwisha.
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Je kuna mtu anaweza kumfundisha Mungu maarifa kwa kuwa yeye huwaukumu hata walio juu?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Mtu mmoja ufa katika nguvu zake kamili, akiwa na utulivu kabisa na kwa amani.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Mwili wake hauna uhitaji, na kiini cha mifupa yake ina unyevu na afya njema.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Mtu mwingine ufa kwa uchungu wa nafsi, bila kujifurahisha kwa jambo lolote jema.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Wanazikwa kaburini wote kwa pamoja, funza wanawafunika wote.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Tazama, nayajua mawazo yenu, na jinsi mnavyotaka kunikosesha.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Kwa kuwa mwasema, 'Iko wapi sasa nyumba ya mwana wa mfalme? Liko wapi kao alipokaa mwovu?'
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Je hamjawauliza wasafiri? Hamfahamu wanavyoweza kusema,
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 kwamba mwovu anaepushwa na siku ya shida, na kwamba anawekwa mbali na siku ya gadhabu?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Ni nani atakaye ituhumu siku ya mwovu mbele yake? Ni nani atakayemwadhibu kwa alichokifanya?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Hata hivyo atapelekwa kaburini; watu wataliona kaburi lake.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Udongo wa bondeni utakuwa mtamu kwake; watu wote watamfuata, hata kuwe na watu wengi mbele yake.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Ni jinsi gani basi mtanifariji bila kufikiri, kwa kuwa majibu yenu hayana lolote ila uongo?”
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Ayubu 21 >